• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juriyar Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya 

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

A cewar babban taron ayyukan raya tattalin arziki na shekara-shekara na kasar Sin da aka gudanar a makon da ya gabata, kasar Sin ta kara inganta manufofinta a bana, don tinkarar tasirin abubuwan da suka wuce yadda ake tsammani da kiyaye zaman lafiyar tattalin arziki da zamantakewar al’umma baki daya, wanda hakan ya kasance wata nasara mai wahalar gaske, bisa ga tsarin da aka tsara. 

Babbar kasuwa, da ingantaccen ci gaban tattalin arziki da inganta yanayin kasuwanci, ya sa dimbin al’ummomin kasa da kasa suna yin tururuwa zuwa kasuwannin kasar Sin, tare da ninka ayyukansu da kara zuba jari, duk da yadda yanayin zuba jari ke ciki a duniya.

  • Jimillar Jarin Da Asusun Raya Kasashen Sin Da Afirka Ya Zuba Ta Zarce Dalar Amurka Biliyan 5 

Alkaluman hukuma sun nuna cewa, a cikin watanni 10 na farkon wannan shekara, jarin kai tsaye da aka zuba a babban yankin kasar Sin ya karu da kaso 14.4 bisa 100 kan makamancin lokaci na shekarar da ta gabata, zuwa yuan triliyan 1.09.

Bangaren masana’antun fasaha, ya ba da rahoton samun ci gaba mai armashi, inda jarin kai tsaye da aka zuba a fannin, ya karu da kashi 57.2 cikin 100 bisa makamancin wannan lokacin.

Bugu da kari, cinikayyar ketare na kasar ya ci gaba da habaka. Babbar hukumar kwastam ta bayyana cewa, a tsakanin watan Janairu zuwa Nuwamba, cinikin kayayyakin ketare na kasar, ya karu da kaso 8.6 bisa dari kan makamancin lokacin shekarar da ta gabata zuwa Yuan triliyan 38.34.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

A wani mataki na daidaita tsarin masana’antu a duniya, birane da dama na kasar Sin, sun fadada ayyukan sufuri da kaddamar da sabbin hanyoyin zirga-zirgar jiragen sama, da na ruwa kai tsaye, don saukaka zirga-zirgar mutane da kayayyaki ta kan iyaka, ta yadda za a karfafa cinikayyar kasa da kasa da farfadowar harkoki a duniya.

Kasar Sin ta taimaka wajen rage hauhawar farashin kayayyaki a duniya ta hanyar karfafa juriyar masana’antu da samar da kayayyaki. (Ibrahim)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa
Daga Birnin Sin

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Next Post
Yadda Kudin Da Ake Karba A Boye Ke Korar Yara Daga Makaranta A Yankin Abuja

Yadda Kudin Da Ake Karba A Boye Ke Korar Yara Daga Makaranta A Yankin Abuja

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.