• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kade-Kaden Symphony Ta Philadelphia Na Ba Da Gudummawa Waje Inganta Abokantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kade-Kaden Symphony Ta Philadelphia Na Ba Da Gudummawa Waje Inganta Abokantakar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 10 ga watan Nuwamba, an gudanar da kade-kade na tunawa da cika shekaru 50 da ziyarar kungiyar kade-kaden Symphony ta Philadelphia a kasar Sin, a gidan wasan kwaikwayo na kasar Sin, tun daga shekarar 1973, kungiyar ta ba da muhimmiyar gudummawa wajen kara fahimtar juna da abokantaka a tsakanin Sin da Amurka.

A shekara ta 1973, kungiyar kade-kaden Symphony ta Philadelphia ta ziyarci kasar Sin a karon farko, kuma ta zama “wakiliyar al’adu” wadda ta karfafa dangantakar Sin da Amurka a tarihi. Tun bayan wannan lokacin, kungiyar ta ziyarci kasar Sin har sau 12, ba wai kawai ta shaida gagarumin sauye-sauye a fannin kade-kade na kasar Sin ba, har ma ta karfafa abokantaka a tsakanin Sin da Amurka.

  • Kwamitin Sulhun MDD Ya Kira Taron Gaggawa Kan Yanayin Da Palastinu Da Isra’ila Ke Ciki
  • Kasar Sin Na Adawa Da Duk Wani Abu Da Zai Yi Illa Ga Fararen Hula Da Keta Dokokin Kasa Da Kasa

Dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka ta kara tabarbarewa matuka tun bayan da Amurka bisa son ra’ayinta ta kaddamar da yakin cinikayya da kasar Sin a shekarar 2018, lamarin da ya jawo matukar damuwa daga al’ummomin duniya game da “sabon yakin cacar baki”.

A watan Nuwamban shekarar 2022, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden a birnin Bali na kasar Indonesiya, inda shugabannin kasashen biyu suka yi tattaunawa mai zurfi ta sahihanci, bisa manyan tsare-tsare kan manyan batutuwan da suka shafi dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, da fatan samun zaman lafiya da ci gaban duniya.

A ‘yan watannin baya-bayan nan, manyan jami’an gwamnatin Amurka sun ziyarci kasar Sin sau da dama, lamarin da ya haifar da karuwar huldar da ke tsakanin sassan biyu, da kuma karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu sannu a hankali.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Farfado da dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, ya kuma sa kaimi ga maido da mu’amalar jama’a tsakanin Sin da Amurka, tare da taka muhimmiyar rawa wajen daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata.

A daren bikin tunawa da cika shekaru 50 da ziyarar kungiyar kade-kaden Symphony ta Philadelphia a kasar Sin, ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, bisa gayyatar da aka yi masa, shugaba Xi Jinping zai tafi birnin San Francisco na kasar Amurka, don gudanar da taron gudanar da shawarwari tare da shugaban Amurka, da kuma halartar kwarya-kwaryar taron koli karo na 30 na kungiyar APEC, ke nan dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka ta shiga “Lokacin San Francisco” a hukumance.

Hakan dai ya samu ne bayan da kasashen biyu suka cimma matsaya kan “Komawa Bali”, amma cimma manufar “Lokacin San Francisco” ba za ta zo da sauki ba.

Kamar yadda wasu masana suka yi nuni da cewa, sabuwar huldar da ke tsakanin kasashen Sin da Amurka ta cewa, duniya ba ta zama karkashin ikon Amurka kadai ba, yayin da ake fuskantar karuwar tasirin da kasar Sin ke da shi a duniya, dole ne Amurka ta nemi sabbin hanyoyin yin zaman tare da kasar Sin.

Jama’a da dama na fatan dangantakar kasar Sin da Amurka za ta iya fitowa daga cikin “yanayi mai sanyi” a dalilin bikin kade-kade na tunawa da cika shekaru 50 da ziyarar kungiyar kade-kaden Symphony ta Philadelphia a kasar Sin, ya kamata kasashen biyu su kiyaye wannan lokaci na annashuwa da aka samu ba cikin sauki ba, da yin aiki tare don samun ci gaba tare, ta hakan za a guji sake samun tabarebarewar dangantakar dake tsakaninsu. (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaMDDSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Tiriliyan 45 Daga Harajin Kaya A 2026

Next Post

Mata A Nemi Sana’a Kuma A Yi Addu’a – Asma’u Kabir

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

2 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

3 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

4 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

5 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

6 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

8 hours ago
Next Post
Mata

Mata A Nemi Sana’a Kuma A Yi Addu’a – Asma’u Kabir

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.