• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar yada labarai ta CGTN ta gudanar ta yanar gizo ya nuna cewa, kashi 93.1 cikin kashi 100 na wadanda suka amsa tambayoyin, sun yi ammana cewa, ya kamata a samu tsaro a yankin Asiya da tekun Pasifik ta hanyar tattaunawar siyasa, inda suka bayyana adawa da yunkurin kafa NATO irin na Asiya.

Adadin mutanen da suka musu tambayoyin da ra’ayin da suka bayyana, tamkar amsa kuwwa ce ga ra’ayi da kiran da kullum Sin ke yi na a warware matsaloli da sabani ta hanyar tattaunawa. Ya kuma kara bayyana kyamar da galibin al’ummomin duniya ke yi da yake-yake da muradinsu na son zaman lafiya. Sai dai, wannan ra’ayi ya bambanta da na wasu ’yan tsiraru dake neman tada rikici ta kowanne hali.

Rikicin da har yanzu yake ci yake cinyewa tsakaninn Ukraine da Rasha, wani gargadi ne cewa, irin wannan yunkuri a yanayin da ake ciki yanzu a duniya, bai kamata ma ya taso ba, muddun ana son tabbatuwar zaman lafiya da kwanciyar hankali, domin jefa duniya zai yi cikin karin tashin hankali.

Kafa kananan rukunonin kawance ko na taron dangi, ba zai haifar da komai ba face rarrabuwar kawuna da kara tsananta sabanin da ake fuskanta, maimakon yunkurin da ake yi na samar da fahimtar juna tsakanin mabambantan al’ummomin duniya da zummar samar da al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil adama.

Duniya ta sauya, kan kasashe ya waye, don haka babu wata kasa da za ta amince da babakere ko mulkin mallaka. Tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe ko wani yanki, ba zai haifar da da mai ido ba. Kasashen dake yankin Asiya da Pasifik, suna da kamanceceniya ta fuskar yanayin rayuwa da al’adu da muradu da sauransu. Haka kuma, su suka san gwagwarmayar da suka yi ta samun ’yanci da matsayin da suka kai a yanzu, don haka, babu wanda ya fi su sanin hanyar warware sabanin dake akwai tsakaninsu domin cimma zaman lafiya, kuma hanya daya tilo ita ce tattaunawa da tuntubar juna a siyasance. (Faeza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinGazaYakin Isra’ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Kimiyya Da Fasaha Zai Taimakawa Afirka Wajen Samun Ci Gaba

Next Post

Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci

Related

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

11 minutes ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Daga Birnin Sin

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

2 hours ago
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

20 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

22 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

23 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

1 day ago
Next Post
Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci

Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da 'Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta'addanci

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.