Kaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Ahmed Musa, ya yi kira ga shugabannin siyasar kasar da su gaggauta dakile tashe-tashen hankula a jihar Benuwe. Musa, wanda ya yi Allah wadai da kashe-kashen da ake yi a jihar kwanan nan, ya kuma bukaci shugabannin da su dauki kwakkwaran mataki don hana ci gaba da zubar da jini a jihar.
A cikin wata sanarwa da ya dora a shafinsa na X, kaftin din na Super Eagles ya bayyana matukar damuwarsa game da karuwar tashe tashen hankula, yana mai bayyana hare-haren a matsayin “wani abu mai kona zuciya” Musa ya rubuta “Mutane nawa ne za a rasa kafin a dauki mataki na gaske, ba za mu iya ci gaba da yin Allah wadai da tashin hankali sannan mu ci gaba ba, kada mu jira har sai abin ya faru kusa da gida ko kuma ga wani da kuka sani kafin ku dauki matakin da ya dace”.
- 2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
Dan wasan na kungiyar Kano Pillars ya jaddada bukatar daukar matakan da suka dace daga shugabanni, inda ya bayyana cewa, “Mulki ba kawai lokacin zabe ba ne, muna bukatar aiyuka akai-akai, Benuwe ta cancanci zaman lafiya, Nijeriya ta cancanci zaman lafiya”, in ji shi.
Daga karshe Musa ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin na baya-bayan nan, inda ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda lamarin ya shafa.
Rahotanni sun nuna cewa sama da mutane 200 ne aka kashe a wani hari da aka kai a Yelwata da ke karamar hukumar Guma, wanda galibi ya hada da ‘yan gudun hijirar da ke neman mafaka a wani cocin Katolika na yankin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp