• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kallon-Kallo: Ƙungiyar Ƙwadago Da ‘Yan Nijeriya

by Muktar Anwar
4 months ago
in Siyasa
0
Kallon-Kallo: Ƙungiyar Ƙwadago Da ‘Yan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba wani abu ne ba sabo mutum ya ji mabanbantan ra’ayoyi da al’umar Nijeriya ke da su game da babbar Kungiyar Kwadago ta Kasa, wato NLC. Babu shakka, ra’ayoyin, kan yi hannun riga ne da juna, sakamakon wasu dalilai da ya kamata a nazarce su da idon basira. Wasu mutane, kan zargi kungiyar ne da raunanan hujjoji, amma dalilan wasu mutanen na sukar kungiyar, sun fi gaban a yi watsi da su cikin kwandon shara. Cikin nazartar wannan dan rubutu, sai Soja ya zamto malamin kansa, ma’ana, sai a ciza ne kuma a hura ido bude!!!.

Samuwar Kungiyar Kwadago (NLC) A Najeriya

Daga dan tarihin da ya zo hannu, an haife wannan kungiya ta kwadago ne cikin Watan Disambar Shekarar 1978, sakamakon maja ko a ce kawance da aka yi tsakaninta da wasu mabanbantan kungiyoyin ‘yan kasuwa da na ma’aikata a Kasar. Tamkar irin yadda aka yi auren siyasar da wasu ke masa kallon auren mutu’a da ya afku a Shekarar 2015 a tsakanin manyan jam’iyyu da kanana a Najeriya, dab da aiwatar da zaben da ya yi silar faduwar gwamnatin PDP, yayinda shugaba Goodluck ya ci damarar yin ta-zarce, daga zangon mulkinsa na daya zuwa na biyu.

  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Kwararrun Yan Kwadago 62,000 Nan Da Shekarar 2035
  • Kamfanin ‘Promasidor Nigeria’ Ya Kaddamar Da Sabuwar Garabasar ‘Onga Taste The Millions Promo’

Daga cikin kungiyoyin da wannan shahararriyar kungiya ta NLC ta yi wancan kawance da su bayan baiyanarta, sun hadar da kungiyar NTUC (Nigeria Trade Union Congress), LUF (Labour Unity Front), ULC (United Labour Congress, da kuma kungiyar NWC (Nigeria Workers Council). Wadannan kungiyoyi hudu ne mafiya girma a wancan lokacin gabatar da yanayin hadakar, amma, akwai wasu kungiyoyin ma’aikatan masana’antu akalla guda arba’in da biyu (42) da suka aiyana danfaruwarsu da ita kungiyar ta NLC a lokacin kafuwar tata.

Bayan kafuwar kungiyar ta NLC, daga shugabancinta na farko, akwai da yawan mutane da suka fito daga wadancan manyan kungiyoyi hudu da aka lasafta a sama (NTUC, LUF, ULC sannan NWC). Wahab Goodluck ne shugabanta da yai silar samuwarta.

Labarai Masu Nasaba

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

Arangama Tsakanin NLC Da Gwamnatocin Soji

Ga duk mutumin da yai duba na tsanaki ga hakikanin manufofin samar da wannan kungiya ta NLC, la-budda, wajibi ne a rika samun sa-toka-sa-katsi tsakaninta da gwamnatoci musamman irin na Soja. Ba kawai gwamnatocin soja ba, da tafiya ta kara nikatawa kamar yadda za a gabatar nan gaba cikin wannan dan rubutu, an wayigari hatta gwamnatocin farar hula ma ba sa wanyewa lafiya da wannan madigar kungiya ta NLC.

A mabanbantan lokutan gwamnatocin Soji a wannan Kasa, an sha yin kwalli da kai farmaki tare da kame shugabannin wannan kungiya ta NLC, inda za a ga cewa, gwamnatocin, sun fi yin amfani ne da jami’an tsaro na farin kaya (DSS), wajen kai hare haren ga ‘yan kungiyar. Bugu da kari, fakam da yawa, jami’an tsaro kan tarwatsa tarukan ganawa da shugabannin kungiyar ke yi a tsakaninsu. Irin wannan kai sammaci ga’yan kungiyar, ya fi afkuwa ne a lokacin da masu bakin kaki (soja) ke jan ragamar Kasar.

Karkashin mulkin soja a Kasa, ta tabbata cewa, sau biyu ne gwamnatocin soja ke sanya kafa su ce sun ma rushe shugabancin kungiyar ta NLC na kasa kacokan. Ba don komai ba, sai don fito na fito ne da kungiyar ke yi game da wasu manufofin gwamnati da suke fassara su da ba alheri ba ne ba ga al’umar Najeriya, gabanin su fara warware alolarsu da tusa!!!.

Cikin Shekarar 1988 ne gwamnatin Soja karkashin mulkin Janar Ibrahim Badamasi Babangida, IBB, aka fara shelanta ruguje shugabancin kungiyar ta NLC. Ba don komai ba, sai don kin goyon bayansu ga wata manufar tattalin arziki da gwamnatin ta samar, wadda aka fi sani da SAP (Structural Adjustment Program). Jin haushin rashin samun goyon bayan NLCn ne ya jaza aiyana soke shugabancinta da gwamnatin IBB ta yi.

Cikin Shekarar 1994 ma, gwamnatin Soja karkashin Janar Sani Abacha, an soke shugabancin kungiyar ta NLC, ba don komai ba, sai don dagewa tare da kumajin kungiyar cewa, lallai ne Kasar ta Nijeriya da ta gaggauta komawa bisa turbar dimukradiyya, sai hakan ya zamto wani babban zunubin da zai wajabta yi wa jagorancin kungiyar rusau. Sannan, wata kitimurmura ta gwamnatocin Soja shi ne, a duk sa’adda suka rushe shugabancin kungiyar na kasa, sai kuma su nadawa kungiyar wani kantoma, don ci gaba da tafiyar da lamuran kungiyar, cikin salon da zai dace da soye-soyen zukatan masu damara, wato Soja.

Cikin Watan Janairun Shekarar 1999, bayan dawowar tsarin mulki irin na dimukradiyya a Kasar ne aka sami sukunin yin wasu gyare-gyare na musamman game da wasu dokoki da suke yin karen-tsaye ga kungiyar ta NLC a lokutan Soja. A wannan lokaci ne aka zabi tsohon gwamna Adams Oshiomhole a matsayin sabon shugaban kungiyar.

Ja-injar NLC Da Gwamnatocin Farar Hula

Tarihin Kungiyar ta NLC bai nuna cewa kawai tsakaninta da gwamnatocin Soja ne ba ta sami rashin fahimtar juna, sam, hatta tsakaninta da masu jagorantar mulkin dimukradiyya a Kasar sun kai ruwa rana! Lokaci ne da Kungiyar ke kan sharafinta da karsashinta, tare da samun kyakkyawar shaida daga akasarin jama’ar Kasa.

A farko farkon Shekarar 2000, an sami wata takaddama tsakanin kungiyar ta NLC da gwamnatin Obasanjo, ba don komai ba, sai don tashin farashin man fetur a Kasar. Wanda hakan ya faru ne sakamakon yunkurin gwamnati na rage adadi mai yawa na tallafi ga man fetur, tare da sallada yin farashin na mai a hannun ‘yan kasuwa’yan jari hujja. Nan take kungiyar ta NLC ta bazama daukar matakan yajin aiki a kai a kai cikin Kasa, a kan hanyarta na tilasa gwamnati yin mi’ara koma baya ga wannan sabuwar manufa tata na rage wani abu daga tallafin na fetur, tare da sallamawa masu manyan masu hada hadar man fetur din a Kasar, jan akalar sanya farashin feturin irin yadda suka so.

Cikin Watan Satumbar Shekarar 2004, kungiyar ta kwadago, ta bai wa gwamnatin Obasanjo wani wa’adin kididdigaggun kwanaki, na, ta canja matsayarta na sanya wani haraji a kan man fetur, ko kuma Kasar ta fuskanci wani gagarumin yajin aiki, duk da cewa wata babbar Kotun taraiya ta fadi cewa, kungiyar ta NLC ba ta da wani hurumi a doka da za ta yi shelar tafiya yajin aiki, kawai don wata manufa da gwamnati ta samar, duk da haka amma, kungiyar NLC, ta shelantawa jama’ar Kasa irin tsare-tsarenta game da tsunduma yajin aikin. A karshe dai jami’an tsaro na farin kaya ne aka yi zargin sun yi ciki da shugaban kungiyar na kasa Oshiomhole, wato sun kame shi.

Sai dai an hakkake cewa, mafi gawurtar zanga-zangar da kungiyar ta yi ita ce ta cikin Watan Janairun Shekarar 2012, a lokacin gwamnatin shugaba Jonathan. Yayinda ya tasamma bin shawarar babban kwamitinsa na tattalin arziki, inda suka hakkake cewa, Kasa na kan tafka asarar biliyoyin nairori game da sha’anin sanya tallafin man feturin. Sannan, aka ga cewa, bayan cire tallafin na mai, farashin litar mai ma zai tashi daga naira sittin da biyar (N 65) zuwa naira dari da arba’in da daya (N 141).

Wancan matsayi da gwamnatin Jonathan ke kokarin dauka, ya jaza kaurewar mummunar zanga-zanga a biranen Lagos da Kano da Fatakwal da sauransu. Wannan irin zanga-zanga da ba a taba gani ba, ta yi silar durkushewar duk wasu sha’anonin tattalin arzikin Kasa. Ala-tilas, sai da shugaba Jonathan ya baiyana yin wurgi da wannan manufa tasa a kafafen yada labarai sannan lamura suka kyautatu, game da wannan zanga-zanga da ake ta faman gabatarwa a cikin sakuna da lungunan Kasar.

Nan da nan mutum ba shi da ikon yankewa wannan kungiya ta NLC hukunci, ba tare da sanin irin nauyayen da ke bisa wuyayenta ba. Bugu da kari, Kungiyar, kan saka jama’ar kasa cikin wasu duffai a wasu lokuta, ta fuskanci kokarin dabbaka hukunci ga wata gwamnati, alhali sun shigar da irin wancan hukunci a mala, sa’adda suka fuskanci wata gwamnatin, alhali nau’in zunubinsu iri guda ne. Yayinda aka fara yin dalla dalla cikin lamuran Kungiyar a nan gaba, akwai yiwuwar mai karatu zai fi fahimtar inda aka sa gaba, ko a ce indagizo ke sakar!!!.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwadagoNigeria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Taimakawa Shirye-shiryen Zabe A Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya

Next Post

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (8)

Related

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 
Siyasa

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

21 hours ago
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Siyasa

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

1 day ago
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya
Siyasa

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

1 day ago
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

3 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

3 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

3 days ago
Next Post
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (8)

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (8)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.