• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanonin EV Na Kasar Sin Ba Sa Dogaro Da Tallafi

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kamfanonin EV Na Kasar Sin Ba Sa Dogaro Da Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wang Wentao, ministan kasuwanci na kasar Sin ya bayyana a jiya Lahadi cewa, saurin bunkasuwar kamfanonin kera motocin lantarki (EV) na kasar Sin, sakamakon kirkire-kirkiren fasahohin zamani ne, da kyakkyawan tsarin samar da kayayyaki, da ingantacciyar takara a kasuwa, ba tallafi ba. Zargin da Amurka da Turai ke yi na samar da motocin fiye da kima ba shi da tushe, a cewarsa.

Zargin da Washington da Turai suka yi na barazanar “girman karfin masana’antun” na kasar Sin wajen samar da hajoji fiye da kima da kuma zargin rashin adalcin cinikayya da kamfanonin Amurka da Turai, ya samo asali ne daga maganganunsu masu tayar da hankali da kuma zurfin rashin fahimta game da kasuwar kasar Sin. Amurka na ganin cewa sassan tattalin arzikin kasar Sin na samun goyan baya da tallafi na wucin gadi, kuma yana rage damammakin ga bunkasuwar kasuwannin Amurka har ma da kawar da ayyukan yi. Yayin da a hakikanin gaskiya, kasar Sin ba ta taba tsunduma cikin harkokin cinikayyar da ba ta dace ba ko nuna son kai ga kamfanoni ba. Kasar Sin ita ce jagora a fannin samar da motocin lantarki wato EV, na’urorin hasken rana, batura, saboda kwarewarta da dorewar sabbin kirkire-kirkirenta, da karuwar bukatun hajojinta daga ko’ina cikin duniya. Hajojin kasar Sin masu inganci suna da fifiko sosai a kasuwannin duniya kuma suna biyan bukatun abokan cinikayya a ketare.

  • Gwamnan Bauchi Ya Bai Wa Ma’aikatan Jihar Goron Sallah Na N10,000 Ga Kowanne
  • Roxy Danckwerts: Ina Matukar Son Rungumar Pandar Kasar Sin

Duk wanda ya lura da karfin tattalin arzikin kasar Sin, ko shakka babu zai fahimci cewa, kasar na bin tsarin ‘yancin cinikayya, da ka’idojin WTO, da tsarin cinikayya na duniya. Kasar Sin ba za ta taba yin amfani da dabarun kasuwancin da ba su dace a kan kamfanonin ketare ko kuma ta yi babakere ba.

Ban da haka, bunkasuwar masana’antun EV na kasar Sin ta ba da muhimmiyar gudummawa wajen tinkarar sauyin yanayi a duniya, da samar da sauye-sauye don kiyaye muhalli da rage hayakin Carbon mai dumama yanayi. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Betta Edu: An Kwato Naira Biliyan 30, An Sanya Asusun Banki 50 Cikin Bincike – EFCC

Next Post

An Amsa Tambayoyi Game Da Ziyarar Da Sakatariyar Baitil-malin Amurka Ta Gudanar A Sin

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

5 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

6 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

6 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

10 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

12 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

13 hours ago
Next Post
An Amsa Tambayoyi Game Da Ziyarar Da Sakatariyar Baitil-malin Amurka Ta Gudanar A Sin

An Amsa Tambayoyi Game Da Ziyarar Da Sakatariyar Baitil-malin Amurka Ta Gudanar A Sin

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.