• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar A Ji Tsoron Aikace-Aikacen Kasar Amurka

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kar A Ji Tsoron Aikace-Aikacen Kasar Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da kasar Amurka ta dakatar da ba da tallafi, kafofin watsa labaru na Najeriya da sauran kasashe dake nahiyar Afirka sun bayyana damuwa kan karancin kudin gudanar da ayyukan kiwon lafiya a kasashensu, da nuna takaici kan yadda gwamnatin kasar Amurka ta dauki mataki ba tare da lura da nauyin dake wuyanta ba. Sai dai idan mu duba kewayenmu, to, za mu ga ashe ba mutanen Afirka kadai ke nuna damuwa da takaici a wannan karo ba.

A nahiyar Turai, kasar Amurka ta yi wa tsoffin kawayenta kasashen Turai kakkausan suka, sa’an nan ta fara shawarwari da kasar Rasha su biyu kadai, lamarin da ya zama juya baya ga kasashen kungiyar EU da Ukraine, ganin yadda wadannan kasashe suka taka muhimmiyar rawa a yakin Rasha da Ukraine, karkashin jagorancin kasar Amurka din.

  • Ƴansanda Sun Kama  Ɓarayin Waya Masu Amfani Da Keke Napep A Adamawa
  • Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga Kan Jami’an NSCDC A Katsina

A nahiyar Amurka kuma, kasar Amurka ta ce za ta mamaye kasar Canada, da neman mallakar koramar Panama, da tsibirin Greenland, ta yadda ta sanya makwabtanta da dama karkashin barazanar kwace yankunansu.

Kana a nahiyar Asiya, Amurka ta ce za ta karbi ikon mulkin yankin Gaza, da korar Falasdinawa daga yankin, maganar da ta fusata dimbin kasashe masu bin addinin Islama.

Haka zalika, ta hanyar kaddamar da yakin harajin kwastam, kasar Amurka ta lahanta moriyar kasashen Canada, da Mexico, da Sin, da Jamus, da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

To, ma iya cewa kasar Amurka ta riga ta fusata dukkan kasashen duniya. Idan an sa wata kasar dake nahiyar Afirka fuskantar matakin da kasar Amurka ta dauka ita kadai, to, za ta ji akwai matsin lamba. Sai dai yanzu za a saki jiki, saboda ko da yake kasar Amurka ta kan ci zarafin sauran kasashe, amma ba ta da karfin cin zarafin dukkan kasashe a sa’i daya. Wannan shi ne dalilin da ya sa ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a wajen taron aikin tsaro na Munich da ya gudana a kwanan nan, cewa bai kamata a ji tsoron aikace-aikacen kasar da ta ke ta nuna fin karfi a duniya ba, saboda galibin kasashen duniya dake tsayawa kan adalci da hadin kai za su cimma nasara a karshe.

Ban da halartar taron tsaro a Munich a wannan karo, Wang Yi ya kuma shugabanci taron kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya, da halartar taron ministocin waje na rukunin kasashe 20 (G20), duk a kwanakin baya. Inda ya jaddada manufofin Sin na aiwatar da ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tsayawa kan daidaituwa, da adalci, da hadin kai, gami da neman zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna, da dai sauransu. Mahalarta tarukan sun nuna yabo kan jawaban ministan na kasar Sin, ganin yadda maganarsa ta kwantar da hankalinsu. Saboda ta nuna cewa, kasar Sin har kullum tana samar da tabbaci ga tsare-tsaren duniya, da ba da gudunmowa a kokarin tabbatar da ci gaban harkokin duniya.

Ban da haka, Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Angola, dake shugabantar kungiyar kasashen Afirka ta AU a karba-karba, Tete Antonio. Inda Wang ya ce, “‘Yan uwa Sinawa dake nahiyar Afirka sun san wace ce kawa ta gaske ta Afirka. “Wannan wata tsohuwar magana ce, amma yanzu ta nuna ma’ana mai zurfi.

Haka zalika, Wang ya ce, “A yunkurin kasashen Afirka na raya kai a nan gaba, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin ba da taimako a matsayin wata sahihiyar abokiya.” Tabbas, za a iya tabbatar da makomar Afirka mai haske, bisa hadin kanta da kasar Sin, da huldar cude-ni-in-cude-ka dake tsakanin daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: NNPP Ta Dakatar Da Sanata Kawu Sumaila Da Wasu ‘Yan Majalisa Uku

Next Post

Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne – Shugaban APC Na Kano

Related

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

9 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

10 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

12 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

13 hours ago
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya
Daga Birnin Sin

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

14 hours ago
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

16 hours ago
Next Post
Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne – Shugaban APC Na Kano

Ministan Gidaje, Ba Ɗan Jam’iyyar APC Ba Ne - Shugaban APC Na Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.