ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kar Turai Ta Yi Watsi Da Damar Daidaita Takaddamarta Da Sin Kan Motoci Masu Amfani Da Lantarki 

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Turai

Ranar 20 ga wata, kwamitin kungiyar Tarayyar Turai EU ya kaddamar da bayanan da suka shafi hukuncin karshe da ya yanke kan yin bincike dangane da kin ba da tallafi kan motoci masu amfani da wutar lantarki na kasar Sin, inda ya shawarci a dora haraji na 17% zuwa 36.3% cikin tsawon shekaru 5 kan motocin da Sin da EU suka kera a kasar Sin. Idan za a aiwatar da irin wannan matakin ba da kariyar ciniki a hukumance, za a haifar da babbar illa ga muradun masana’antun motocin kasar Sin, da hadin gwiwar Sin da EU ta fuskar tsarin samar da kaya mai ruwa da tsaki, lamarin da zai yi illa ga ita kanta EU.

 

Tun daga ranar 21 ga watan Yunin bana har zuwa yanzu, Sin da EU sun yi tattaunawa har sau fiye da 10 dangane da takaddamarsu kan motocin masu amfani da lantarki. Amma EU ba ta tanadi shawarar Sin cikin bayananta ba, ba ta gyara kuskurenta ba. EU ta yanke hukuncin ne bisa gaskiyar da ita kanta ta amince da ita, a maimakon gaskiyar da Sin da EU duka suka amince da ita. Lamarin ya saba wa abun da wasu Turawa suka bayyana, wato mutunta ka’idoji, tafiyar da harkoki bisa doka da yin adalci.

ADVERTISEMENT

 

Ainihin hadin kan Sin da EU shi ne neman samun moriyar juna da nasara tare. Har kullum kasar Sin tana nuna sahihanci, tana himmantuwa wajen yin tattaunawa da EU don daidaita takaddamar ciniki. Amma Sin ba za ta kau da kai daga yadda aka illata muradunta ba. Ba za ta sadaukar da muradunta sakamakon matakan ba da kariyar ciniki ba. A ranar 9 ga watan da muke ciki, kasar Sin ta gabatar da kara dangane da matakin EU ga hukumar ciniki ta duniya WTO, matakin da ya nuna cewa, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka wajaba domin kiyaye muradun kamfanonin kasarta. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Da Matakan Saukaka Matsi Daga Bashin Dake Wuyansu

Sin Na Taimakawa Kasashen Afirka Da Matakan Saukaka Matsi Daga Bashin Dake Wuyansu

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.