• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kara Kakabawa Saura Haraji—Matakin Farfado Da Masana’antun Amurka Ko Girbar Abin Da Take Shukawa?

by Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kara Kakabawa Saura Haraji—Matakin Farfado Da Masana’antun Amurka Ko Girbar Abin Da Take Shukawa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da dama zababben shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ambaci kafa “Zamanin zinari” a Amurka, tun bayan da ya sake darewa ragamar mulkin kasar, har ma ya ce shugaban kasar na 25 William Mckinley ya samar da manyan sauye-sauye ga Amurka bisa matakan haraji da ya dauka. To amma abun tambaya a nan shi ne shin matakin haraji da Trump ya dauka zai iya farfado da masana’antun kasarsa ko zai haifar da sabanin hakan—wato girbar abun da ya shuka.

A karni na 19, ko da yake dokar haraji ta Mckinley da ta Dingley sun taimakawa Amurka wajen sauya salonta daga kasa mai dogaro kan aikin gona zuwa kasa mafi karfi a bangaren masana’antu. Amma, illolli sun faru yayin da ake aiwatar da ita, daga cikinsu illa mafi tsanani ita ce hauhawar farashi. Alkaluma na nuna cewa, daga shekarar 1897 zuwa 1907, yawan kudaden da al’ummar kasar suka kashe a yau da kullum ya karu da kashi 33%. A sa’i daya kuma, buga karin harajin da Amurka ta yi ya haifar da gogayyar ciniki tsakanin kasa da kasa. Hakan ya sa, shahararren mai nazarin tarihin tattalin arziki na Amurka Douglas A. Irwin ya ce, matakin harajin da aka dauka a wannan zamanin da ake kira “Zamani mai feshin ruwan zinariya” ba ya haifar da tasiri mai amfani ko mummunar illa.

  • Ofishin Siyasa Na Kwamitin Tsakiyar Jks Ya Kira Taron Nazarin Ayyukan Kiyaye Muhallin Halittu Da Sauransu
  • Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Hadin Gwiwar Inganta Amfani Da AI Don Amfanar Da Kowa

Sai dai a wannan karnin da muke ciki na 21, yadda Trump ke kwaikwayon Mckinley da nufin kafa “Zamani na zinari”, zai habaka mummunan illolin da matakan haraji ke haifarwa, a maimakon farfado da masana’antun kasar.

Daukar matakan haraji ba za su kai ga warware matsalolin da ake fuskanta ta fannin sana’o’in samar da kayayyaki a cikin gidan kasar Amurka ba. Shafin yanar gizo na jaridar Financial Times ta Birtaniya ya ba da labari kwanan baya cewa, manufofi marasa tabbaci na gwamnatin Amurka, da ma rashin samun kudaden tallafawa, har da rashin kwadago da sauransu matsaloli ne da Amurka ke fuskanta, kuma sun hana bunkasar masana’antun kasar. Gwamnatin Trump na matukar son daidaita wadannan matsaloli bisa matakan haraji kadai, amma ba za ta cimma nasara ba ko kadan. A maimakon haka, Amurka na shan dacin wannan mataki——kafofin yada labarai kamar su CBS sun ba da labari cewa, a ran 25 ga watan nan da muke ciki kawancen manyan kamfanonin kasa da kasa na Amurka da aka san shi da sunan “Conference Board” ya gabatar da rahoton ma’aunin CCI da ta shaida kwarin gwiwar masu sayayya, wanda ya nuna cewa CCI na Amurka na kara raguwa a wannan wata. Ban da wannan kuma, masu nazarin tattalin arziki na Goldman Sachs sun rage hasashen da suka yi wa saurin bunkasuwar GDPn Amurka a karshen rubu’in shekarar 2025 daga 2.2% zuwa 1.7%. A sa’i daya kuma, kasashe da dama na daukar matakin haraji don mai da martani kan Amurka. Amurka tana mayar da kanta saniyar ware ke nan.

Kasancewar kasa da kasa na kara cude-ni-in-cude-ka a hada-hadar cinikayya da tsarin samar da kayayyaki, wanda hakan ke bukatar hadin gwiwar kasa da kasa, kuma Amurka na mai da kanta saniyar ware, ta kuma girbi abun da take shukawa, bisa matakan kariyar ciniki da ta dauka. (MINA)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar Aikin Ceto Ta Kasa Da Kasa Ta Kasar Sin Ta Isa Myanmar

Next Post

Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Related

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

20 hours ago
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

21 hours ago
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara
Daga Birnin Sin

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

22 hours ago
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

23 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

24 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

1 day ago
Next Post
Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

September 5, 2025
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.