• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Fu Cong ya koka game da yadda batun Falasdinu ya zamowa duniya “kadangaren bakin tulu”, inda ya yi kashedin cewa, a kullum tashin hankali a Gaza na ci gaba da tsawaita, tare da hallaka karin fararen hula, a gabar da cikakken yaki ke neman barkewa a Gabas ta Tsakiya baki daya.

 

Tabbas rikicin Palasdinu da Isra’ila da aka shafe tsawon shekara guda yana gudana, ya zama wani muhimmin batu dake jan hankalin al’ummar duniya. Batun kare hakkin bil adama da na wanzar da zaman lafiya da kullum kasashen duniya ke furtawa, ya zama wani abu da yanzu ake amfani da shi a matsayin makami na siyasa da nuna fuska biyu da kuma haifar da wariya, maimakon ainihin ma’anarsa.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Rundunar CPG Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

Manyan kasashen duniya kan fake da batun ne idan suna da wani muradi da suke son cimmawa ko kuma neman shafa bakin fenti kan wasu kasashe. Yadda wasu kasashen ke mayar da hankali wajen kakkaba takunkumi ko yayata karairayi game da batun hakkin bil adama, abun takaici ne, la’akari da yadda suka yi biris ko ma suke kara rura wutar take hakkin mutane masu rauni a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Dukkanin bil adama na da hakkin da ya kamata a kare, haka kuma suna da ’yancin rayuwa. Daukar bangaranci a wannan rikici da kullum ke kara habaka, ba zai amfanawa duniya da komai ba sai karin rarrabuwar kawuna da tsana da rikici.

 

Kamata ya yi kasashen da suke ganin kansu manya ne, su karkatar da lokaci da karfi da ma albarkatun da suke zubawa wajen yada jita-jita da karairayi, wajen kai dauki ga masu rauni da kuma lalubo mafita mai dorewa ga wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

 

Babu wanda zai tsira idan wani sashe na duniya na fama da rikici. Don haka, lokaci ya yi da ya kamata a daina nuna bangaranci, a hada hannu da kasashe masu kaunar zaman lafiya kamar Sin, dake kira da a shawo kan rikicin ta hanyar tattaunawa da lumana da samar da mafita da za ta karbu ga dukkan bangarori domin hankalin kowa ya kwanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji

Next Post

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Related

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

7 hours ago
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

8 hours ago
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

9 hours ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

10 hours ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

11 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

12 hours ago
Next Post
Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.