• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Fu Cong ya koka game da yadda batun Falasdinu ya zamowa duniya “kadangaren bakin tulu”, inda ya yi kashedin cewa, a kullum tashin hankali a Gaza na ci gaba da tsawaita, tare da hallaka karin fararen hula, a gabar da cikakken yaki ke neman barkewa a Gabas ta Tsakiya baki daya.

 

Tabbas rikicin Palasdinu da Isra’ila da aka shafe tsawon shekara guda yana gudana, ya zama wani muhimmin batu dake jan hankalin al’ummar duniya. Batun kare hakkin bil adama da na wanzar da zaman lafiya da kullum kasashen duniya ke furtawa, ya zama wani abu da yanzu ake amfani da shi a matsayin makami na siyasa da nuna fuska biyu da kuma haifar da wariya, maimakon ainihin ma’anarsa.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Rundunar CPG Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

Manyan kasashen duniya kan fake da batun ne idan suna da wani muradi da suke son cimmawa ko kuma neman shafa bakin fenti kan wasu kasashe. Yadda wasu kasashen ke mayar da hankali wajen kakkaba takunkumi ko yayata karairayi game da batun hakkin bil adama, abun takaici ne, la’akari da yadda suka yi biris ko ma suke kara rura wutar take hakkin mutane masu rauni a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

Dukkanin bil adama na da hakkin da ya kamata a kare, haka kuma suna da ’yancin rayuwa. Daukar bangaranci a wannan rikici da kullum ke kara habaka, ba zai amfanawa duniya da komai ba sai karin rarrabuwar kawuna da tsana da rikici.

 

Kamata ya yi kasashen da suke ganin kansu manya ne, su karkatar da lokaci da karfi da ma albarkatun da suke zubawa wajen yada jita-jita da karairayi, wajen kai dauki ga masu rauni da kuma lalubo mafita mai dorewa ga wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

 

Babu wanda zai tsira idan wani sashe na duniya na fama da rikici. Don haka, lokaci ya yi da ya kamata a daina nuna bangaranci, a hada hannu da kasashe masu kaunar zaman lafiya kamar Sin, dake kira da a shawo kan rikicin ta hanyar tattaunawa da lumana da samar da mafita da za ta karbu ga dukkan bangarori domin hankalin kowa ya kwanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji

Next Post

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Related

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

54 minutes ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

2 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

3 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

4 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

23 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

24 hours ago
Next Post
Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.