• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kare Hakki Da Rayukan Mutane Ba Batu Ne Na Siyasantarwa Ko Nuna Fuska Biyu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin din-din-din na kasar Sin a MDD Fu Cong ya koka game da yadda batun Falasdinu ya zamowa duniya “kadangaren bakin tulu”, inda ya yi kashedin cewa, a kullum tashin hankali a Gaza na ci gaba da tsawaita, tare da hallaka karin fararen hula, a gabar da cikakken yaki ke neman barkewa a Gabas ta Tsakiya baki daya.

 

Tabbas rikicin Palasdinu da Isra’ila da aka shafe tsawon shekara guda yana gudana, ya zama wani muhimmin batu dake jan hankalin al’ummar duniya. Batun kare hakkin bil adama da na wanzar da zaman lafiya da kullum kasashen duniya ke furtawa, ya zama wani abu da yanzu ake amfani da shi a matsayin makami na siyasa da nuna fuska biyu da kuma haifar da wariya, maimakon ainihin ma’anarsa.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Rundunar CPG Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Jihar
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Likitan Mata A Zamfara

Manyan kasashen duniya kan fake da batun ne idan suna da wani muradi da suke son cimmawa ko kuma neman shafa bakin fenti kan wasu kasashe. Yadda wasu kasashen ke mayar da hankali wajen kakkaba takunkumi ko yayata karairayi game da batun hakkin bil adama, abun takaici ne, la’akari da yadda suka yi biris ko ma suke kara rura wutar take hakkin mutane masu rauni a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

Labarai Masu Nasaba

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Dukkanin bil adama na da hakkin da ya kamata a kare, haka kuma suna da ’yancin rayuwa. Daukar bangaranci a wannan rikici da kullum ke kara habaka, ba zai amfanawa duniya da komai ba sai karin rarrabuwar kawuna da tsana da rikici.

 

Kamata ya yi kasashen da suke ganin kansu manya ne, su karkatar da lokaci da karfi da ma albarkatun da suke zubawa wajen yada jita-jita da karairayi, wajen kai dauki ga masu rauni da kuma lalubo mafita mai dorewa ga wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

 

Babu wanda zai tsira idan wani sashe na duniya na fama da rikici. Don haka, lokaci ya yi da ya kamata a daina nuna bangaranci, a hada hannu da kasashe masu kaunar zaman lafiya kamar Sin, dake kira da a shawo kan rikicin ta hanyar tattaunawa da lumana da samar da mafita da za ta karbu ga dukkan bangarori domin hankalin kowa ya kwanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji

Next Post

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Related

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

17 hours ago
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

18 hours ago
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

19 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

20 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

21 hours ago
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

2 days ago
Next Post
Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

Fu Cong: Kasar Sin Tana Goyon Bayan MDD Don Kara Himma Da Inganci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.