• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Kasa

Bayan Lesotho, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya samu karin wata kasar da bai san ta ba a duniya.

 

A ganawarsa da firaministar kasar Italiya Giorgia Meloni a kwanan baya, shugaba Trump ya ce bai san komai ba game da Congo, duk da cewa ana samun bakin haure da yawa a Amurka wadanda suka fito daga kasar. “Akwai su masu yawan gaske da suka zo daga Congo. Ban san mene ne wannan ba, amma sun zo ne daga Congo da ma sauran sassan duniya.”

  • Arsenal Da PSG: Wa Zai Yi Nasara A Gasar Zakarun Turai A Yau?
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Jamhuriyar dimokuradiyyar Congo ce shugaba Trump yake nufi, kasar da ta kasance mafi girma ta biyu a duniya, wadda ke da yawan al’ummar da ya zarce miliyan 100.

 

LABARAI MASU NASABA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

Ba wannan ne karo na farko da shugaba Trump ya nuna girman kai da rashin sani game da Afirka ba. A watan da ya gabata, lokacin da yake bayani game da dalilin da ya sa gwamnatinsa ke rage gudummawar jin kai da take bayarwa a duniya, ya ce a baya, Amurka ta samar wa kasar Lesotho gudummawar dala miliyan 8, amma “ba wanda ya taba jin sunan wannan kasa”. Amma ita wannan kasar da ko sunanta shugaba Trump bai taba ji ba, ya sanya ta cikin jerin kasashen da ya sanar da zai kakaba musu haraji, har ma ya sanya mata haraji na kaso 50%. Idan ba mu manta ba kuma, a wa’adin shugabancinsa na farko, shugaba Trump ya taba bayyana kasashen Afirka a matsayin “shithole” a lokacin da ya tabo maganar bakin haure.

 

Sai dai ban da girman kai da rashin sani, kalaman shugaba Trump ya kuma bayyana matsayin da gwamnatin kasar Amurka ta dade tana dauka a game da kasashen Afirka, wato a maimakon abokan hadin gwiwa na zaman daidaito da martaba juna, tana kallonsu a matsayin abin da take iya amfani da su wajen takara da sauran manyan kasashe, kuma muna iya ganin haka ne daga manufofin da mahukuntan kasar suka dauka cikin ‘yan shekarun baya.

 

A shekarar 2014, gwamnatin Barack Obama ta shirya taron kolin Amurka da kasashen Afirka karo na farko, inda ta dauki alkawura a gaban kasashen Afirka. Sai dai bayan taron, a maimakon ta kara samar da gudummawa, sai ta rage, har da kudaden da take samarwa a fannin yaki da cutar kanjamau a Afirka. A gun taron, Amurka ta kuma yi alkawarin zurfafa huldarta da kasashen Afirka da ma gudanar da taron a kai a kai, amma ba a sake yin taron ba har sai bayan tsawon shekaru 8. A karshen shekarar 2022, Amurka ta gudanar da taron karo na biyu, inda tsohon shugaban kasar Joe Biden ya yi alkawarin samar da iya abin da kasarsa take iya bayarwa don tabbatar da kyautata makomar Afirka, kuma a cewarsa zai kai ziyara Afirka a shekarar 2023, amma bai cika wannan alkawari ba sai zuwa karshen bara, lokacin da ya kusan sauka daga kujerar shugabanci, kuma ba mu san yaushe za a cika sauran alkawuran da ya dauka ba.

 

Bayan da gwamnati mai ci ta fara aiki, jerin matakan da ta dauka sun haifar da munanan illoli ga kasashen Afirka. In mun dauki misali da harajin kwastam na ramuwar gayya da ta dauka a baya bayan nan, inda ta sanya haraji mai yawa kan kasashen Afirka 51, ciki har da 50% a kan Lesotho da 47% a kan Madagascar da 40% a kan Mauritius, matakin da ya kasance tamkar yi wa kasashen fashi. Abin lura kuma shi ne, harajin ya dakatar da dokar samar da ci gaba da damammaki a Afirka da aka san ta da AGOA, tun kafin wa’adinta ya cika, lamarin da ya jefa kasashen Afirka da dama cikin mawuyacin hali wajen yin ciniki da Amurka.

 

Har kullum kasar Sin na ganin cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, a maimakon wajen yin takara tsakanin manyan kasashe. Rashin girmamawa ne ga kasashen Afirka da al’ummarsu yadda Amurka take da rashin sanin nahiyar, kuma rashin sahihancin da take wa hadin gwiwarta da kasashen Afirka ya shaida gazarwata ta daukar kasashen Afirka da muhimmanci. Kasashen Afirka na bukatar kawaye na gaske. Idan gwamnatin Trump tana son samun karbuwa daga kasashen Afirka, dole ne ta gyara matsayinta, kuma ya kamata ta fara da fahimtar kowace kasa da ke nahiyar. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Binciken Yawaitar Haɗurran Tankokin Man Fetur A Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

Magance Bala’o’i: Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudirin Gwamnatin Zamfara Na Ci Gaba Da Haɗin Gwiwa Da NEMA

October 13, 2025
Asuu

Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 

October 13, 2025
hisba

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

October 13, 2025
Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Nijeriya

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

October 13, 2025
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

October 13, 2025
nema

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya

October 13, 2025
Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.