• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kariyar Cinikayya Ba Za Ta Hana Sin Cimma Burinta Na Samun Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kariyar Cinikayya Ba Za Ta Hana Sin Cimma Burinta Na Samun Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin kolin JKS da majalisar gudanarwar kasar, sun fitar da wasu ka’idoji da burikan kare muhalli a jiya Litinin, wato zuwa 2030, kasar za ta cimma nasarori a fannin sauya akala zuwa ci gaba maras gurbata muhalli, a dukkanin fannonin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Kana zuwa 2035, ta cimma burin fitar da iskar carbon mafi karanci. 

 

Batun sauyin yanayi wani muhimmin batu ne da ya addabi duniya. Kuma kasar Sin ta kasance gaba-gaba wajen ganin tabbatuwar muradin duniya na shawo kan sauyin yanayi ta hanyoyi daban-daban, duk kuwa da cikas din da wasu ke kawowa wannan yunkuri.

  • Tawagar JKS Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Rwanda
  • Anya Nahiyar Afirka Fili Ne Na Gudanar Da Takara?

Hakika ni ganau ce na irin nasarorin da Sin take samu wajen neman ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba. Daga lokacin da na zo kasar zuwa yanzu, na ga yadda a wani lokaci a da can, sararin samaniya ke dusashewa saboda hayakin masana’antu, amma zuwa yanzu, wannan ya zama labari, domin kwata-kwata sararin samaniya a washe take a ko da yaushe, inda na kan yi mamakin yadda a hankali a hankali aka samu wannan gagarumin sauyi. Baya ga wannan, kasar Sin na kokarin kare muhalli da yaki da hayakin carbon ta hanyar shuka bishiyoyi, domin na gani da idona yadda hamada ta zama dausayi. Haka kuma na ga yadda ababen hawa masu amfani da makamashi mai tsafta ke mamaye titunan kasar a hankali.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Hakika dabarun da kasar Sin take amfani da su abun burgewa ne da koyi. Misali, yayin da ake rajin shuka bishiyoyi, ana karfafawa mutane gwiwar shuka bishiyoyi masu samar da kudin shiga, domin samun riba biyu. Haka kuma yayin da ake raya masana’antar ababen hawa masu amfani da makamashi mai tsafta, an tanadarwa jama’a rangwame wajen sayen irin wadannan motoci, har ma a wasu yankuna, a kan ba da damar sauya tsoffin motoci masu amfani da man fetur da masu amfani da lantarki kan farashi mai rahusa.

 

Sai dai kuma duk da wannan yunkuri da irin ci gaba na a zo a gani da take samu, maimakon a yaba ko a yi koyi da ita, wasu kasashe na kokarin kawo cikas. Amma a tunanina, cikas din da suke kawowa ba ga kasar Sin ba ne, cikas ne ga duniya da za su iya amfana da dabaru da kayayyakin kasar Sin masu kare muhalli. Kuma ina da yakinin cewa, kasar Sin ta yi a gaba a wannan fanni, kana matakan kariyar cinikayya ba za su hana zuwa wadancan shekaru da Sin ta dibarwa kanta, ta cimma burinta na sauyawa baki daya, zuwa ga samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Cinikin Hajojin Da Ba A Gama Sarrafa Su Ba Tsakanin Sin Da Afirka Ya Karu Da Kashi 6.4 A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Next Post

FRSC Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 16 A Wani Haɗarin Motoci A Hanyar Legas

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano

FRSC Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 16 A Wani Haɗarin Motoci A Hanyar Legas

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.