• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Kasar Sin na kafa ‘tarkon bashi’ a Afirka, tana kafa ‘sabon salon mulkin mallaka’……” A cikin ’yan shekarun baya bayan nan, kafofin yada labarai na kasashen yamma sun sha yayata irin wadannan karairayi, a kokarin lalata huldar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka da ma hadin gwiwarsu.

Kaza lika a kwanakin baya, irin wadannan kafofi sun kara fitar da wani tsokacin, inda jaridar “The Times” ta Burtaniya, a wani rahotonta mai taken “Sinawa na ba ’yan tawayen Najeriya rashawa, don neman mallakar albarkatun ma’adinai”, ta zargi kasar Sin da “samar da kudin tallafi ga harkokin ta’addanci a Najeriya.”

  • Richard Sears: Harufan Sinanci Ba Kawai Na Kasar Sin Ba Ne, Al’ada Ce Mai Daraja Ga Duniya Baki Daya

Rahoton dai ya yi matukar jawo hankalin al’ummar Najeriya, har ma wasu da suke shan wahalar ta’addanci, da ma hare-haren ’yan tawaye sun fara nuna shakku ga hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. A game da hakan, Ambassada Isma’il Ahmed, mai sharhi kan harkokin diplomasiyya a Najeriya, a yayin tattaunawa da mu ya yi nuni da cewa, “ba wai wani abun mamaki ba ne don sun yi amfani da kafafen yada labaransu, ko jaridu wajen sukar China, ai sun sha yi.”

Ambassada Isma’il Ahmed ya ce, “A cikinsu guda hudu kamar Sudan, Aljeriya, Najeriya da Masar, dukkanninsu za ka ga suna da man fetur, kuma China na sayen fetur daga wajensu, don haka dole Turawa su ta da hankalinsu, kuma har gobe tagomashi ake samu ta fuskar cinikayya da tattalin arziki. Duk kamfanonin da suke Najeriya yanzu, suke ayyukan gine-ginen hanyoyin mota, da na layin dogon jiragen kasa, da tasoshin jiragen sama, dukkan kamfanoni ne na China, saboda sun fi sauki, sun fi dadin alaka, sun fi amana, sun fi gudanar da komai ba tare da an sa siyasa a ciki ba. Saboda haka zai yi wahala nan gaba a ce wai Turawa za su samu hanyoyin da ake tunanin za su yi amfani da su, domin fitar da kasar China daga hulda da kasashen Afrika.

Yawanci su kasashen Turawa suna amfani da damar su ce wajen daurewa masu mulkin kama-karya gindi, su yi ta mulkin mallaka a kasashen Afirka, amma ka kula abubuwa suna ja baya a yanzu, masu mulkin mallakar su kan kare, kuma su kansu su kan karkata su koma bangaren China.”

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

To kamar dai yadda Ambassada Isma’il Ahmed ya fada, kasashen Afirka a matsayinsu na kasashe masu mulkin kai, suna da kwarewa wajen yanke shawara, kan ko hadin gwiwarsu da wata kasa na da amfani ko illa, kuma suna da ’yancin zabar abokan hadin gwiwa, kuma in an yi nazari, a cikin ’yan shekarun baya, hadin gwiwar cin moriyar juna a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya samar da kyawawan sakamako na a zo a gani.

A karshe wannan rahoto na “The Times”, ya ce, “Najeriya kamar za ta ci gaba da zabar kasar Sin ta fannin zuba mata jari a maimakon kasashen yamma. Bayan ziyarar da mataimakiyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris ta kai Afirka a wannan wata, mataimakin shugaban Nijeriya Yemi Osinbajo, ya yaba da alfanun da aka samu bisa ga tallafin da kasar Sin ta samar, kuma shi ma zababben shugaban Najeriya mai jiran gado Bola Ahmed Tinubu, tuni ya zanta da jakadan kasar Sin.”

A hakika, kullum kasar Sin tana maraba da sassan kasa da kasa, da su aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, kuma sau tari ta sha bayyana cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasashen duniya, a maimakon fagen takarar manyan kasashe.

Karya dai fure take ba ta ’ya’ya, wadanda suke makircin lalata hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, muna ba su shawarar mai da hankalinsu a kan taimakawa kasashen Afirka, wajen tabbatar da ci gabansu a maimakon su rika yayata karairayi. Kasar Sin na maraba da karin kasashe su sa hannu a ayyukan raya Afirka, amma kuma tana adawa da niyya, da matakai na shafawa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka bakin fenti. Baya ga haka, muna kuma jan hankalin abokanmu na Nijeriya, da kada su fada cikin tarkon da kasashen yamma suka dana na dakile bunkasuwarsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri A Fadar Gwamnati A Abuja.

Next Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Related

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

1 hour ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

2 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

20 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

21 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

22 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

23 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.