• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Kasar Sin na kafa ‘tarkon bashi’ a Afirka, tana kafa ‘sabon salon mulkin mallaka’……” A cikin ’yan shekarun baya bayan nan, kafofin yada labarai na kasashen yamma sun sha yayata irin wadannan karairayi, a kokarin lalata huldar da ke tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka da ma hadin gwiwarsu.

Kaza lika a kwanakin baya, irin wadannan kafofi sun kara fitar da wani tsokacin, inda jaridar “The Times” ta Burtaniya, a wani rahotonta mai taken “Sinawa na ba ’yan tawayen Najeriya rashawa, don neman mallakar albarkatun ma’adinai”, ta zargi kasar Sin da “samar da kudin tallafi ga harkokin ta’addanci a Najeriya.”

  • Richard Sears: Harufan Sinanci Ba Kawai Na Kasar Sin Ba Ne, Al’ada Ce Mai Daraja Ga Duniya Baki Daya

Rahoton dai ya yi matukar jawo hankalin al’ummar Najeriya, har ma wasu da suke shan wahalar ta’addanci, da ma hare-haren ’yan tawaye sun fara nuna shakku ga hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. A game da hakan, Ambassada Isma’il Ahmed, mai sharhi kan harkokin diplomasiyya a Najeriya, a yayin tattaunawa da mu ya yi nuni da cewa, “ba wai wani abun mamaki ba ne don sun yi amfani da kafafen yada labaransu, ko jaridu wajen sukar China, ai sun sha yi.”

Ambassada Isma’il Ahmed ya ce, “A cikinsu guda hudu kamar Sudan, Aljeriya, Najeriya da Masar, dukkanninsu za ka ga suna da man fetur, kuma China na sayen fetur daga wajensu, don haka dole Turawa su ta da hankalinsu, kuma har gobe tagomashi ake samu ta fuskar cinikayya da tattalin arziki. Duk kamfanonin da suke Najeriya yanzu, suke ayyukan gine-ginen hanyoyin mota, da na layin dogon jiragen kasa, da tasoshin jiragen sama, dukkan kamfanoni ne na China, saboda sun fi sauki, sun fi dadin alaka, sun fi amana, sun fi gudanar da komai ba tare da an sa siyasa a ciki ba. Saboda haka zai yi wahala nan gaba a ce wai Turawa za su samu hanyoyin da ake tunanin za su yi amfani da su, domin fitar da kasar China daga hulda da kasashen Afrika.

Yawanci su kasashen Turawa suna amfani da damar su ce wajen daurewa masu mulkin kama-karya gindi, su yi ta mulkin mallaka a kasashen Afirka, amma ka kula abubuwa suna ja baya a yanzu, masu mulkin mallakar su kan kare, kuma su kansu su kan karkata su koma bangaren China.”

Labarai Masu Nasaba

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

To kamar dai yadda Ambassada Isma’il Ahmed ya fada, kasashen Afirka a matsayinsu na kasashe masu mulkin kai, suna da kwarewa wajen yanke shawara, kan ko hadin gwiwarsu da wata kasa na da amfani ko illa, kuma suna da ’yancin zabar abokan hadin gwiwa, kuma in an yi nazari, a cikin ’yan shekarun baya, hadin gwiwar cin moriyar juna a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya samar da kyawawan sakamako na a zo a gani.

A karshe wannan rahoto na “The Times”, ya ce, “Najeriya kamar za ta ci gaba da zabar kasar Sin ta fannin zuba mata jari a maimakon kasashen yamma. Bayan ziyarar da mataimakiyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris ta kai Afirka a wannan wata, mataimakin shugaban Nijeriya Yemi Osinbajo, ya yaba da alfanun da aka samu bisa ga tallafin da kasar Sin ta samar, kuma shi ma zababben shugaban Najeriya mai jiran gado Bola Ahmed Tinubu, tuni ya zanta da jakadan kasar Sin.”

A hakika, kullum kasar Sin tana maraba da sassan kasa da kasa, da su aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka, kuma sau tari ta sha bayyana cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasashen duniya, a maimakon fagen takarar manyan kasashe.

Karya dai fure take ba ta ’ya’ya, wadanda suke makircin lalata hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, muna ba su shawarar mai da hankalinsu a kan taimakawa kasashen Afirka, wajen tabbatar da ci gabansu a maimakon su rika yayata karairayi. Kasar Sin na maraba da karin kasashe su sa hannu a ayyukan raya Afirka, amma kuma tana adawa da niyya, da matakai na shafawa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka bakin fenti. Baya ga haka, muna kuma jan hankalin abokanmu na Nijeriya, da kada su fada cikin tarkon da kasashen yamma suka dana na dakile bunkasuwarsu. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Da Tinubu Sun Yi Ganawar Sirri A Fadar Gwamnati A Abuja.

Next Post

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Related

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

2 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

3 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

4 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

6 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

1 day ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

1 day ago
Next Post
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Da A Martaba Ka’idojin Cinikayya Maras Shinge

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.