• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Ba Da Shawarwari 6 Game Da Matakan Tsaro Yayin Tattaunawar Shangri-La

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Ba Da Shawarwari 6 Game Da Matakan Tsaro Yayin Tattaunawar Shangri-La
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Lahadi ne ministan tsaron kasar Sin Dong Jun, ya gabatar da muhimmin jawabi a gun taron tattaunawar Shangri-La karo na 21 da aka yi a kasar Singapore, inda ya mai da hankali kan ra’ayin kasar Sin dangane da tabbatar da tsaron duniya. 

Dong ya ce, a wannan gabar da duniya ke fuskantar sauye-sauye, yana da matukar muhimmanci a kafa wani sabon tsarin hadin gwiwar tsaron yanki, wanda zai tabbatar da daidaita damar tofa albarkacin baki ga kasashen duniya, da kaucewa fadace-fadacen kungiyanci, da samar da mu’amala ta gaske, da sada zumunci da gaskiya kuma cikin daidaito.

  • Na’urar Chang’e-6 Ta Kasar Sin Ta Sauka A Gefen Wata Mai Nisa Don Tattara Samfura
  • Wang Yi Ya Gana Da Bakin Kasashen Larabawa Da Suka Halarci Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Hadin-kan Kasar Sin Da Kasashen Larabawa

Bisa wannan dalili ne kasar Sin ta gabatar da shawarwari guda shida, wadanda suka hada da kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya, da samar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa, da yin amfani da tsarin tsaron shiyya-shiyya yadda ya kamata, da inganta hadin gwiwar tsaro bisa gaskiya kuma a aikace, da kafa misali a hadin gwiwar tsaron teku, da kuma inganta tafiyar da harkoki a yankuna masu bukatar tsaro.

Game da batun Taiwan, Dong Jun ya bayyana cewa, rundunar ‘yantar da jama’ar kasar Sin PLA a ko da yaushe ta kasance wani karfi wajen kare dinkuwar kasar Sin. PLA za ta dauki kwararan matakai don dakile neman ‘yancin kai na Taiwan da tabbatar da cewa irin wannan makircin ba zai yi nasara ba.

Dong Jun ya ci gaba da cewa, kasar Sin ta yi kira da a hada kai don samar da zaman lafiya, kana tana adawa da kulla kebabben kawancen soja dauke da mummunar manufa. Ya ce, “kananan kawance” daban daban dake harin wasu kasashe ba za su iya tabbatar da zaman lafiya a yankin ba, sai dai su haifar da karin tashin hankali.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

Ya kara da cewa, sojojin kasar Sin za su dauki karin matakai a bayyane, da yin aiki tare da sojojin dake kasashen yankin, wajen gina wani sabon nau’in hadin gwiwar tsaro dake nuna daidaito, da amincewa da juna, da hadin gwiwar samun nasara tare.

Dong Jun ya kuma bayyana cewa, kasar Sin na kara azama kan yin shawarwarin zaman lafiya bisa kyakkyawan nufi kan rikicin Ukraine, kuma ba ta taba bayar da makamai ga kowane bangare na rikicin Ukraine ba. (Yahaya)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tada Rikicin Yankin Tekun Kudancin Sin Shi Ne Makarkashiyar Amurka

Next Post

An Ceto Ragowar Ɗaliban Jami’ar Da Aka Yi Garkuwa Da Su Jihar Kogi

Related

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU

15 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI 

16 hours ago
Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba
Daga Birnin Sin

Alakar Sin Da EU Na Bukatar Hadin Gwiwa Ba Raba-gari Ba

17 hours ago
Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

18 hours ago
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

19 hours ago
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

20 hours ago
Next Post
Sin

An Ceto Ragowar Ɗaliban Jami'ar Da Aka Yi Garkuwa Da Su Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Wutar lantarki

Arewa Maso Gabas Ce Za Ta Biya Kudin Wuta Mafi Tsada A Sabon Tsarin Lantarki

July 25, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

July 25, 2025
Manzon Allah

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)

July 25, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

‘Yan Nijeriya Miliyan 40 Ke Fuskantar Barazanar Kwararowar Hamada – Ministan Muhalli

July 25, 2025
Shugaban Hukumar DSS Ya Kaddamar Da Cibiyar Koyar Da Addinin Musulunci A Kaduna 

Matsalar Tsaro: Sarakuna Sun Bukaci Gwamnati Ta Canza Salo

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.