• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Ba Da Shawarwari 6 Game Da Matakan Tsaro Yayin Tattaunawar Shangri-La

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Ba Da Shawarwari 6 Game Da Matakan Tsaro Yayin Tattaunawar Shangri-La
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Lahadi ne ministan tsaron kasar Sin Dong Jun, ya gabatar da muhimmin jawabi a gun taron tattaunawar Shangri-La karo na 21 da aka yi a kasar Singapore, inda ya mai da hankali kan ra’ayin kasar Sin dangane da tabbatar da tsaron duniya. 

Dong ya ce, a wannan gabar da duniya ke fuskantar sauye-sauye, yana da matukar muhimmanci a kafa wani sabon tsarin hadin gwiwar tsaron yanki, wanda zai tabbatar da daidaita damar tofa albarkacin baki ga kasashen duniya, da kaucewa fadace-fadacen kungiyanci, da samar da mu’amala ta gaske, da sada zumunci da gaskiya kuma cikin daidaito.

  • Na’urar Chang’e-6 Ta Kasar Sin Ta Sauka A Gefen Wata Mai Nisa Don Tattara Samfura
  • Wang Yi Ya Gana Da Bakin Kasashen Larabawa Da Suka Halarci Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Hadin-kan Kasar Sin Da Kasashen Larabawa

Bisa wannan dalili ne kasar Sin ta gabatar da shawarwari guda shida, wadanda suka hada da kiyaye halaltacciyar moriyar tsaro ta dukkan kasashen duniya, da samar da daidaito da adalci a tsakanin kasa da kasa, da yin amfani da tsarin tsaron shiyya-shiyya yadda ya kamata, da inganta hadin gwiwar tsaro bisa gaskiya kuma a aikace, da kafa misali a hadin gwiwar tsaron teku, da kuma inganta tafiyar da harkoki a yankuna masu bukatar tsaro.

Game da batun Taiwan, Dong Jun ya bayyana cewa, rundunar ‘yantar da jama’ar kasar Sin PLA a ko da yaushe ta kasance wani karfi wajen kare dinkuwar kasar Sin. PLA za ta dauki kwararan matakai don dakile neman ‘yancin kai na Taiwan da tabbatar da cewa irin wannan makircin ba zai yi nasara ba.

Dong Jun ya ci gaba da cewa, kasar Sin ta yi kira da a hada kai don samar da zaman lafiya, kana tana adawa da kulla kebabben kawancen soja dauke da mummunar manufa. Ya ce, “kananan kawance” daban daban dake harin wasu kasashe ba za su iya tabbatar da zaman lafiya a yankin ba, sai dai su haifar da karin tashin hankali.

Labarai Masu Nasaba

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Ya kara da cewa, sojojin kasar Sin za su dauki karin matakai a bayyane, da yin aiki tare da sojojin dake kasashen yankin, wajen gina wani sabon nau’in hadin gwiwar tsaro dake nuna daidaito, da amincewa da juna, da hadin gwiwar samun nasara tare.

Dong Jun ya kuma bayyana cewa, kasar Sin na kara azama kan yin shawarwarin zaman lafiya bisa kyakkyawan nufi kan rikicin Ukraine, kuma ba ta taba bayar da makamai ga kowane bangare na rikicin Ukraine ba. (Yahaya)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tada Rikicin Yankin Tekun Kudancin Sin Shi Ne Makarkashiyar Amurka

Next Post

An Ceto Ragowar Ɗaliban Jami’ar Da Aka Yi Garkuwa Da Su Jihar Kogi

Related

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare
Daga Birnin Sin

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

10 hours ago
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243
Daga Birnin Sin

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

11 hours ago
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

11 hours ago
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

13 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

14 hours ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

1 day ago
Next Post
Sin

An Ceto Ragowar Ɗaliban Jami'ar Da Aka Yi Garkuwa Da Su Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.