A yau Alhamis, ma’aikatar ciniki ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci kasar Amurka da ta yi watsi da amfani da batun tsaron kasa barkatai wadda ta mayar da shi mai gamewa gaba daya da kuma wuce gona da iri, kana ta hada kai da dukkan bangarori wajen kiyaye tsarin cinikayya tsakanin sassa daban-daban.
A wani taron manema labarai da aka saba yi a-kai-a-kai, mai magana da yawun ma’aikatar, He Yongqian, ta bayyana hakan a lokacin da aka bukaci ta tofa albarkacin bakinta game da matakin da Amurka ta dauka na kara haraji kan karafa da holoko da kayayyakin da ake sarrafawa da su wadanda ake kaiwa kasar, daga kashi 25 zuwa 50 cikin dari. Ya ce irin wannan yunkuri na Amurka ba wai yana cutar da wasu da ita kadai ba ne, har ma zai kawo cikas ga sha’anin tafiyar da masana’antu cikin lumana da samar da kayayyaki a duniya.
Lokacin da take tsokaci kan sabbin takunkumai da Amurka ta sanya ga kasar Sin bayan tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi a Geneva cikin watan Mayu, mai magana da yawun ma’aikatar ta ce, kasar Sin ta sauke hakkokinta, tare da tabbatar da aiki da matsayar da aka cimma a tattaunawar.
Sai dai kuma, duk da haka, Amurka ta kakaba wasu sabbin takunkumai kan kasar Sin, tare da yin watsi da matsayar da aka cimma, kuma ta yi mugun tauye hakkoki da muradun kasar Sin. Ta kara da cewa, kasar Sin tana matukar nuna rashin gamsuwa da kuma adawa da hakan, inda ta bukaci Amurka da ta dakatar lamarin nan take. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp