• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Juma’a ne wakilin kasar Sin a MDD ya bukaci Isra’ila da ta aiwatar da kudurin MDD game da tsagaita bude wuta a zirin Gaza daga dukkan fannoni, yana mai cewa, abu mai ban tausayi da ke faruwa a Gaza ya zama gwaji ga lamirin bil Adama da kuma amincin kwamitin sulhu na MDD. 

Mukaddashin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Dai Bing ya bayyana a kwamitin sulhu na MDD a jiya Juma’a cewa, mun bukaci Isra’ila da ta gaggauta aiwatar da kudurin, da kuma dakatar da hare-haren soji da take kaiwa Gaza, da azabtar da fararen hular Gaza.

  • Kasar Sin Ta Ba Da Taimakon Jinya Kyauta Ga Mafiya Rauni Miliyan 250 A shekarar 2023
  • Kasar Sin Na Allah Wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Ma’aikatan Agaji Na Kasa Da Kasa A Gaza

Ya yi tir da harin da Isra’ila ta kai wa motocin jigilar kayayyakin jin kai, ya kuma bukaci Isra’ila da ta mutunta dokokin kasa da kasa da kuma dokokin jin kai na kasa da kasa, da dakatar da kai hare-hare kan hukumomin jin kai da ma’aikata, tare da ba da hadin kai ga hukumomin jin kai don kai agaji.

Dai dai ya jaddada cewa, ta hanyar aiwatar da tsarin samar da “kasashe guda biyu” daga dukkan fannoni da kuma kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta ne, yankin zai iya fita daga cikin mummunan yanayi, inda Isra’ila da Falasdinu suke ta yin rikici a tsakaninsu. Ya nanata matsayin kasar Sin kan goyon bayan Falasdinu ta zama mamban MDD a hukumance, kana ya bukaci kwamitin sulhun da ya dauki mataki cikin gaggawa.

Kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD a jiya Juma’a ya zartas da wani kudiri na neman a dorawa Isra’ila alhakin aikata laifukan yaki da kuma cin zarafin bil’Adama a zirin Gaza. Kudirin ya kuma bukaci dukkan kasashen duniya da su dakatar da sayarwa, da mikawa, da kuma karkatar da makamai da alburusai da sauran kayan aikin soji ga Isra’ila.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Daga cikin kasashe 47 da ke cikin kwamitin, wasu 28 ne suka kada kuri’ar amincewa, 13 ba su kada kuri’a ba, yayin da wasu 6 suka ki amincewa da kudirin. Kasar Sin ta goyi bayan kudirin, yayin da Amurka da Jamus suka nuna adawa da shi. (Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

Next Post

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Related

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

2 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

2 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

14 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

15 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

16 hours ago
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

17 hours ago
Next Post
Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.