• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Juma’a ne wakilin kasar Sin a MDD ya bukaci Isra’ila da ta aiwatar da kudurin MDD game da tsagaita bude wuta a zirin Gaza daga dukkan fannoni, yana mai cewa, abu mai ban tausayi da ke faruwa a Gaza ya zama gwaji ga lamirin bil Adama da kuma amincin kwamitin sulhu na MDD. 

Mukaddashin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Dai Bing ya bayyana a kwamitin sulhu na MDD a jiya Juma’a cewa, mun bukaci Isra’ila da ta gaggauta aiwatar da kudurin, da kuma dakatar da hare-haren soji da take kaiwa Gaza, da azabtar da fararen hular Gaza.

  • Kasar Sin Ta Ba Da Taimakon Jinya Kyauta Ga Mafiya Rauni Miliyan 250 A shekarar 2023
  • Kasar Sin Na Allah Wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Ma’aikatan Agaji Na Kasa Da Kasa A Gaza

Ya yi tir da harin da Isra’ila ta kai wa motocin jigilar kayayyakin jin kai, ya kuma bukaci Isra’ila da ta mutunta dokokin kasa da kasa da kuma dokokin jin kai na kasa da kasa, da dakatar da kai hare-hare kan hukumomin jin kai da ma’aikata, tare da ba da hadin kai ga hukumomin jin kai don kai agaji.

Dai dai ya jaddada cewa, ta hanyar aiwatar da tsarin samar da “kasashe guda biyu” daga dukkan fannoni da kuma kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta ne, yankin zai iya fita daga cikin mummunan yanayi, inda Isra’ila da Falasdinu suke ta yin rikici a tsakaninsu. Ya nanata matsayin kasar Sin kan goyon bayan Falasdinu ta zama mamban MDD a hukumance, kana ya bukaci kwamitin sulhun da ya dauki mataki cikin gaggawa.

Kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD a jiya Juma’a ya zartas da wani kudiri na neman a dorawa Isra’ila alhakin aikata laifukan yaki da kuma cin zarafin bil’Adama a zirin Gaza. Kudirin ya kuma bukaci dukkan kasashen duniya da su dakatar da sayarwa, da mikawa, da kuma karkatar da makamai da alburusai da sauran kayan aikin soji ga Isra’ila.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Daga cikin kasashe 47 da ke cikin kwamitin, wasu 28 ne suka kada kuri’ar amincewa, 13 ba su kada kuri’a ba, yayin da wasu 6 suka ki amincewa da kudirin. Kasar Sin ta goyi bayan kudirin, yayin da Amurka da Jamus suka nuna adawa da shi. (Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Gargadi Manoman Kan Sayar Da Kayan Aikin Da Ta Ba Su

Next Post

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

13 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

14 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

16 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

17 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

18 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

19 hours ago
Next Post
Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.