• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Bukaci Isra’ila Da Ta Aiwatar Da Kudurin MDD Na Tsagaita Bude Wuta A Gaza

by CGTN Hausa
2 years ago
Gaza

A jiya Juma’a ne wakilin kasar Sin a MDD ya bukaci Isra’ila da ta aiwatar da kudurin MDD game da tsagaita bude wuta a zirin Gaza daga dukkan fannoni, yana mai cewa, abu mai ban tausayi da ke faruwa a Gaza ya zama gwaji ga lamirin bil Adama da kuma amincin kwamitin sulhu na MDD. 

Mukaddashin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Dai Bing ya bayyana a kwamitin sulhu na MDD a jiya Juma’a cewa, mun bukaci Isra’ila da ta gaggauta aiwatar da kudurin, da kuma dakatar da hare-haren soji da take kaiwa Gaza, da azabtar da fararen hular Gaza.

  • Kasar Sin Ta Ba Da Taimakon Jinya Kyauta Ga Mafiya Rauni Miliyan 250 A shekarar 2023
  • Kasar Sin Na Allah Wadai Da Harin Da Aka Kai Wa Ma’aikatan Agaji Na Kasa Da Kasa A Gaza

Ya yi tir da harin da Isra’ila ta kai wa motocin jigilar kayayyakin jin kai, ya kuma bukaci Isra’ila da ta mutunta dokokin kasa da kasa da kuma dokokin jin kai na kasa da kasa, da dakatar da kai hare-hare kan hukumomin jin kai da ma’aikata, tare da ba da hadin kai ga hukumomin jin kai don kai agaji.

Dai dai ya jaddada cewa, ta hanyar aiwatar da tsarin samar da “kasashe guda biyu” daga dukkan fannoni da kuma kafa kasar Falasdinu mai cin gashin kanta ne, yankin zai iya fita daga cikin mummunan yanayi, inda Isra’ila da Falasdinu suke ta yin rikici a tsakaninsu. Ya nanata matsayin kasar Sin kan goyon bayan Falasdinu ta zama mamban MDD a hukumance, kana ya bukaci kwamitin sulhun da ya dauki mataki cikin gaggawa.

Kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD a jiya Juma’a ya zartas da wani kudiri na neman a dorawa Isra’ila alhakin aikata laifukan yaki da kuma cin zarafin bil’Adama a zirin Gaza. Kudirin ya kuma bukaci dukkan kasashen duniya da su dakatar da sayarwa, da mikawa, da kuma karkatar da makamai da alburusai da sauran kayan aikin soji ga Isra’ila.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Daga cikin kasashe 47 da ke cikin kwamitin, wasu 28 ne suka kada kuri’ar amincewa, 13 ba su kada kuri’a ba, yayin da wasu 6 suka ki amincewa da kudirin. Kasar Sin ta goyi bayan kudirin, yayin da Amurka da Jamus suka nuna adawa da shi. (Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.