• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Jaddada Muhimmancin Dagewa Nuna Fifiko Ga Ci Gaban Gina Zaman Lafiya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar sin

Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya yi jawabi a gun budadden taron muhawara kan batun samar da zaman lafiya, wanda majalisar ta gudanar a jiya Alhamis 26 ga watan nan, inda ya jaddada cewa, kamata ya yi a nuna fifiko kan samar da ci gaba a yayin da ake raya ayyukan zaman lafiya. 

Zhang Jun ya bayyana cewa, gina zaman lafiya wani muhimmin bangare ne na samar da dauwamammen zaman lafiya, kuma ya fi muhimmanci da yin fice a halin da ake ciki yanzu. Ya kara da cewa, ya kamata aikin samar da zaman lafiya ya karkata ga samar da ci gaba.

  • Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

Ga kasashe da yawa, ci gaba shi ne babbar mafita wajen tinkarar kalubale daban-daban. Akwai bukatar a nuna fifiko kan ci gaba don samar da zaman lafiya, kuma a mai da hankali kan amfani da albarkatu wajen kawar da talauci, da kare rayuwar jama’a, da yada ilimi, da kiwon lafiyar jama’a da sauran fannoni. Kana da nuna goyon baya ga raya masana’antu, da sha’anin noma, da zamanintar da muhimman ababen more rayuwa.

Ya ce kamata ya yi kasashe masu ci gaba su cika alkawuran da suka dauka, na ba da tallafin ci gaba da samar da kudade don shawo kan kalubalen sauyin yanayi, tare kuma da biyan basussukan da suka ci a tarihi.

A nasu bangaren, ya kamata hukumomin hada-hadar kudi na kasa da kasa su sauke nauyin da ya rataya a wuyansu, su shiga cikin aikin samar da zaman lafiya, da gudanar da hadin kai.

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Zhang Jun ya kuma kara bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da ba da goyon baya ga aikin samar da zaman lafiya, ta hanyar aiwatar da hakikanin matakai, da kuma ba da gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya mai dorewa. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
NIS Ta Kubutar Da Mutum 45 Daga Masu Safarar Mutane A Jigawa

NIS Ta Kubutar Da Mutum 45 Daga Masu Safarar Mutane A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
NAWIA

Ranar Abinci Ta Duniya: NAWIA Ta Tallafawa Mata 114  Da Kayan Aikin Gona A Zamfara

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

Tsohon Ɗan Wasan Dambe, Ricky Hatton Ya Rataye Kansa

October 16, 2025
Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

Alkaluman Jin Ra’ayi na CGTN Sun Shaida Amincewar Al’umma Da Karfin Tattalin Arzikin Kasar Sin

October 16, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya

October 16, 2025
Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.