• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Zargin Da Ministocin Kudin Kasashen G7 Suka Yi Mata

by CGTN Hausa
1 year ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Yau Litinin 27 ga wata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta maida martani game da zargin da taron ministocin kudin kasashen G7 ya yi wa kasarta cewa, wai tana aiwatar da manufofi da daukar matakan da ba na kasuwa ba. Jami’ar ta ce, akwai wasu kasashen yammacin duniya kalilan da suke nuna bambancin ra’ayi kan wasu daidaikun kasashe ko daidaikun kamfanoni, al’amarin da ya sabawa ka’idojin kasuwa. Ta ce kasashen G7 na yunkurin rura wutar rikici cewa, wai kasar Sin tana wuce gona da iri wajen samar da hajoji, da zummar kawo cikas ga hajoji masu amfani da sabbin makamashi da kasar Sin ta samar, al’amarin da ya saba wa hakikanin gaskiya da manufar tattalin arziki, kana, mataki ne na bada kariya ga harkokin kasuwanci, wanda bai dace da moriyar kowane bangare ba.

Kaza lika, yayin da take amsa tambayar da aka yi mata, dangane da kalaman da jami’an gwamnatin kasar Amurka suka furta cewa, wai akwai yiwuwar jirgin ruwan kasar Sin mai aikin gyare-gyare, ya yi amfani da layukan sadarwa dake karkashin tekun Fasifik wajen gudanar da aikin leken asiri, Mao Ning ta ce, gwamnatin Amurka tana shafa bakin fenti gami da matsa lamba ga kamfanonin sadarwa na kasar Sin da na sauran kasashe, domin kirkiro wani babban tsarin sa ido a duk duniya, wanda ita Amurka kadai za ta jagoranta, ba tare da abokin gogayya, da sa idon sauran kasashe ba. A cewar kakakin, kasar Sin na shawartar gwamnatin Amurka wadda ke yunkurin kiyaye babakere a harkokin sadarwar yanar gizo ta intanet, da ta dakatar da shafawa kamfanonin kasar Sin bakin fenti, da daina daukar matakin ban dariya, wanda ta ce ya yi kama da “barawo na kiran kama barawo”. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kira Taron Manema Labarai Game Da Halartar Shugaba Xi Jinping Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Tattauna Hadin-Kan Sin Da Kasashen Larabawa

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kira Taron Manema Labarai Game Da Halartar Shugaba Xi Jinping Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Tattauna Hadin-Kan Sin Da Kasashen Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.