• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karfin Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Za Ta Samar Da Karfin Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton da MDD ta fitar a kwanan baya, ya yi hasashen cewa, bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin za ta karu zuwa kaso 4.8% a shekarar 2023, lamarin da zai sa ta zama jagoran bunkasuwar tattalin arzikin shiyyar da kasar Sin take. Ita ma a nata bangare, babbar daraktar kungiyar cinikayya ta duniya WTO madam Ngozi Okonjo-Iweala, a yayin da ta zanta da wakilinmu a kwanan baya, bayan da aka rufe taron dandalin tattalin arzikin duniya a garin Davos na kasar Switzerland, ta ce kasancewarta injin bunkasuwar tattalin arzikin duniya, yadda kasar Sin ta sake bude kofarta ga duniya, mataki ne da zai taimakawa duniya baki daya. 

A hakika, bikin bazara da aka gudanar a kasar Sin a makon da ya gabata ya shaida hasashen da aka yi. Bikin bazara biki ne da al’ummar Sinawa ke yi na murnar sabuwar shekara bisa kalandar gargajiya ta wata, kuma bikin na bana ya kasance na farko da aka yi tun bayan da aka sassauta matakan kandagarkin cutar Covid-19, kuma sakamakon nasarorin da aka cimma cikin shekaru uku da suka wuce ta fannin dakile cutar, a bana, al’ummar Sinawa sun fi gudanar da bikin cikin murna da farin ciki, inda aka ga Sinawa masu yawan gaske na zuwa wuraren shakatawa, da gidajen sinima, da gidajen cin abin da sauransu.

  • Mataimakin Wakilin Kasar Sin Dake MDD Ya Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Taimakawa Mali Kara Karfin Yaki Da Ta’addanci

Alkaluman da aka fitar sun nuna cewa, yawan wadanda suka yi bulaguro a cikin kasar Sin, a lokacin hutun bikin na tsawon mako guda ya kai miliyan 308, adadin da ya karu da kashi 23.1% kan na bara. Kana yawan kudaden shiga da aka samu a fannin ya kai kudin Sin RMB Yuan biliyan 375.8, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 55.52, wanda ya karu da kashi 30% kan na bara. Sa’an nan kuma yawan kudaden tikitin kallon fina-finai a lokacin hutun ya kai yuan biliyan 6.758, wanda ya karu da kaso 11.89 kan na bara. Lallai duk wadannan sun sake shaidawa duniya babbar kasuwar kasar da kuma ingancin tattalin arzikin kasar.

A sa’i daya kuma, bayan da kasar Sin ta sassauta matakan kandagarkin cutar, da kuma maido da bulaguron da ’yan kasar ke yi zuwa ketare, Sinawa da yawa sun kuma tafi yawon shakatawa a kasashen ketare a yayin bikin na bana, kuma alkaluman da aka samar sun shaida cewa, yawan yarjejeniyoyin yawon shakatawa da baki Sinawa suka yi zuwa waje, a bana ya karu da kimanin kaso 640%.

A jajebirin bikin, rukunin baki masu yawon shakatawa na kasar Sin na farko tun bayan da aka sassauta matakan yaki da cutar ya sauka a birnin Alkahira, kuma sassan kula da harkokin yawon shakatawa da kayayyakin tarihi na kasar Masar sun shirya bikin maraba da dawowar bakin a filin jirgin sama. Haka ma lamarin yake a kasashen Switzerland, da Indonesia, da Maldive, da New Zealand da Turkiyya, wadanda suka yi suna ta fannin harkokin yawon shakatawa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Kafofin yada labarai da suka hada da Prensa Latina, da Reuters, da kuma Itar-Tass, sun ba da rahotannin cewa, dawowar baki masu yawon shakatawa daga kasar Sin, za ta taimaka ga farfadowar harkokin yawon shakatawa a duniya baki daya.

Ana fatan alheri ga wannan sabuwar shekarar da aka shiga, kuma tabbas kasar Sin za ta samar da karfin farfado da tattalin arzikin duniya a wannan shekara. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Bunkasa Farfadowar Tattalin Arziki Da Daidaito A Fannin Cinikayyar Waje Da Zuba Jari

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

45 minutes ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

2 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

3 hours ago
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

4 hours ago
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

5 hours ago
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

6 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi

Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa'adin Daina Tsaffin Kudi

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.