• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe Da Dama Sun Amince Da Kafuwar Kasar Falasdinu Yayin Da Amurka Ta Ci Gaba Da Kau Da Kai

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Falasdinu

Ranar 22 ga wata, a babban zauren MDD da ke New York na kasar Amurka, kasashen Faransa, Belgium, Luxembourg da wasu kasashe 3 sun amince da kafuwar kasar Falasdinu a taron manyan jami’ai kan warware batun Falasdinu cikin lumana da aiwatar da shirin kafuwar kasashe 2. Ranar 21 ga wata kuma kasashen Birtaniya, Canada, Australiya, Portugal su ma sun tsai da kuduri iri daya. Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya yi nuni da cewa, “Ya zama tilas mu yi iyakacin kokarin kiyaye yiwuwar shirin kafuwar kasashe 2.” Kana kuma Ursula von der Leyen, shugabar kwamitin kungiyar Tarayyar Turai EU cewa ta yi, EU na mara bayan warware rikicin Falasdinu da Isra’ila bisa shirin kafuwar kasashe 2.

Ya zuwa yanzu kasashe 157 daga cikin 193 mambobin MDD ne suka amince da kafuwar kasar Falasdinu, wadanda yawansu ya wuce kaso 80%. A cikin kasashe 5 masu kujera dindindin a kwamitin tsaron MDD, wasu 4 sun amince da kafuwar kasar ta Falasdinu, wadanda yawansu ya wuce 80%. Ma iya cewa, akasarin kasashen duniya sun amince da kafuwar kasar Falasdinu.

Me ya sa kasashen duniya masu dimbin yawa suka amince da kafuwar kasar Falasdinu a daidai wannan lokaci? Kuka daga zirin Gaza zai ba mu amsa. A cikin rikicin Falasdinu da Isra’ila na wannan zagaye da ya barke a watan Oktoban shekarar 2023, Falasdinawa fiye da dubu 65 sun rasa rayukansu yayin da wasu fiye da dubu 160 suka jikkata cikin matakan soja da Isra’ila take dauka a zirin Gaza.

A sa’i daya kuma, wasu kasashe da dama sun gano cewa, babu wanda zai iya maye gurbin shirin na kafuwar kasashe 2 a fannin warware batun Falasdinu. Ya zama tilas a inganta goyon bayan shirin a siyasance.

Masharhanta sun nuna cewa, yanzu ana mayar da Amurka saniyar ware kan batun Falasdinu da Isra’ila. Wasu kasashen yammacin duniya sun amince da kafuwar kasar Falasdinu sakamakon yadda Amurka ta fara rasa karfin shugabanci a duniya, kana kuma kasashen duniya na kokarin sake fasalin tsarin wanzar da zaman lafiya a duniya. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.