• English
  • Business News
Tuesday, September 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe Da Dama Sun Amince Da Kafuwar Kasar Falasdinu Yayin Da Amurka Ta Ci Gaba Da Kau Da Kai

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashe Da Dama Sun Amince Da Kafuwar Kasar Falasdinu Yayin Da Amurka Ta Ci Gaba Da Kau Da Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 22 ga wata, a babban zauren MDD da ke New York na kasar Amurka, kasashen Faransa, Belgium, Luxembourg da wasu kasashe 3 sun amince da kafuwar kasar Falasdinu a taron manyan jami’ai kan warware batun Falasdinu cikin lumana da aiwatar da shirin kafuwar kasashe 2. Ranar 21 ga wata kuma kasashen Birtaniya, Canada, Australiya, Portugal su ma sun tsai da kuduri iri daya. Shugaba Emmanuel Macron na Faransa ya yi nuni da cewa, “Ya zama tilas mu yi iyakacin kokarin kiyaye yiwuwar shirin kafuwar kasashe 2.” Kana kuma Ursula von der Leyen, shugabar kwamitin kungiyar Tarayyar Turai EU cewa ta yi, EU na mara bayan warware rikicin Falasdinu da Isra’ila bisa shirin kafuwar kasashe 2.

Ya zuwa yanzu kasashe 157 daga cikin 193 mambobin MDD ne suka amince da kafuwar kasar Falasdinu, wadanda yawansu ya wuce kaso 80%. A cikin kasashe 5 masu kujera dindindin a kwamitin tsaron MDD, wasu 4 sun amince da kafuwar kasar ta Falasdinu, wadanda yawansu ya wuce 80%. Ma iya cewa, akasarin kasashen duniya sun amince da kafuwar kasar Falasdinu.

Me ya sa kasashen duniya masu dimbin yawa suka amince da kafuwar kasar Falasdinu a daidai wannan lokaci? Kuka daga zirin Gaza zai ba mu amsa. A cikin rikicin Falasdinu da Isra’ila na wannan zagaye da ya barke a watan Oktoban shekarar 2023, Falasdinawa fiye da dubu 65 sun rasa rayukansu yayin da wasu fiye da dubu 160 suka jikkata cikin matakan soja da Isra’ila take dauka a zirin Gaza.

A sa’i daya kuma, wasu kasashe da dama sun gano cewa, babu wanda zai iya maye gurbin shirin na kafuwar kasashe 2 a fannin warware batun Falasdinu. Ya zama tilas a inganta goyon bayan shirin a siyasance.

Masharhanta sun nuna cewa, yanzu ana mayar da Amurka saniyar ware kan batun Falasdinu da Isra’ila. Wasu kasashen yammacin duniya sun amince da kafuwar kasar Falasdinu sakamakon yadda Amurka ta fara rasa karfin shugabanci a duniya, kana kuma kasashen duniya na kokarin sake fasalin tsarin wanzar da zaman lafiya a duniya. (Tasallah Yuan)

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

Next Post

UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

Related

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

51 seconds ago
Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya
Daga Birnin Sin

Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya

1 hour ago
Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

2 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

3 hours ago
Kasar Sin Ta Mallaki Kusan Tashoshin Fasahar 5G Miliyan 4.65
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Mallaki Kusan Tashoshin Fasahar 5G Miliyan 4.65

6 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

8 hours ago
Next Post
UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau

September 23, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

An Yanke Wa Sojojin Da Suka Sayar Wa ‘Yan Ta’adda Makamai Hukuncin Ɗaurin Rai-da-rai A Borno

September 23, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya

Aikin Ba Da Ilmi Na Tushe Na Kasar Sin Ya Kai Matsakaicin Matsayi Na Kasashe Masu Arziki A Duniya

September 23, 2025
Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

Gavi Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Yi Masa Tiyata

September 23, 2025
Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Ya Isa New York Don Halartar Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 23, 2025
UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya

September 23, 2025
Kasashe Da Dama Sun Amince Da Kafuwar Kasar Falasdinu Yayin Da Amurka Ta Ci Gaba Da Kau Da Kai

Kasashe Da Dama Sun Amince Da Kafuwar Kasar Falasdinu Yayin Da Amurka Ta Ci Gaba Da Kau Da Kai

September 23, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

September 23, 2025
Noma

Babban Bankin Nijeriya Ya Rage Kuɗin Ruwan Da Bankuna Ke Caja

September 23, 2025
Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa

Jihar Kogi Na Cikin Fargaba Yayin Da Kogin Neja Da Benuwe Suka Tumfatsa

September 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.