• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne asusun ba da lamuni na duniya IMF ya sake yin kwaskwarima ga hasashen bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin a shekarar 2024, lamarin dake nuni da cewa tattalin arzikin kasar Sin na iya zarce hasashen da aka yi a baya, duba ga irin gudummawar da ta bayar wajen bunkasar tattalin arzikin duniya a shekarar 2023, wanda ya haura kashi 30 cikin 100, lamarin da ya kara tabbatar da matsayinta ta babbar kasuwa dake bunkasa tattalin arzikin duniya. Wannan kyakkyawar hangen nesa ba wai kawai yana da fa’ida ga kasar Sin ba, har ma zai yi tasiri ga ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, musamman ma kasashe masu tasowa.

Kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa a fannin masana’antu da samar da kayayyaki a duniya. Ta zama cibiyar masana’antu ta duniya, yayin da take jawo hannun jari kai tsaye daga ketare tare da yin amfani da wadatar kwadago mai rahusa da inganci, da inganta ababen more rayuwa, da kwararrun ma’aikata. Kazalika, kwararrun masana’antu na musamman na kasar Sin da ingantattun tsarin samar da kayayyaki sun sa ta zama muhimmin bangare a yawancin masana’antun duniya.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Wasu Ka’idojin Kula Da Muhalli Dake Mayar Da Hankali Kan Yankuna Daban-daban

Kamfanonin kasar Sin na amfani da sabbin dabarun aiki da hidimomi, tare da habaka karfinsu na sarrafa hajoji da hidimomi, da takara mai tsafta, suna zuba jari a kasuwannin kasashen waje. Kuma suna da fa’ida sosai a fannonin da suka hada da fasahohin zamani, da samar da hajoji mara gurbata muhalli, da kuma sauya akalar hada-hadar kasuwanci zuwa dijital. Sun cimma wannan nasarar ne ta hanyar zuba jari a ayyukan kirkire-kirkire a fannonin da suka hada da fasahar 5G, da kirkirarriyar basira (AI), da makamashin da ake sabuntawa, da kuma motocin lantarki wadanda suka jawo hankalin duniya.

A matsayinta na kasar da ta fi fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje, kasar Sin ta kulla huldar kasuwanci mai yawa da kasashen duniya. Alal misali, ayyukanta a karkashin shirin shawarar “ziri daya da hanya daya” (BRI) suna habaka hadin gwiwa da karfafa dangantakar tattalin arziki da kasashe abokan huldarta. Wannan matsayi bisa manyan tsare-tsare ya baiwa kasar Sin damar taka muhimmiyar rawa wajen tsara yanayin cinikayyar duniya da inganta hadin gwiwar tattalin arziki.

Rawar gani da kasar Sin ke takawa a kasuwar duniya ya taimaka dunkule tattalin arzikin duniya. Duniya na tasirantuwa da ci gabanta kamar yadda take ba da kuzari da kwanciyar hankali ga tattalin arzikin duniya, yayin da take more damar samun ci gaba tare da sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Kwato Gidaje 324 Na ‘Yan Fansho Da Aka Karkatar A Jihar Kano

Next Post

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

6 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

8 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

9 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

10 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

11 hours ago
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

13 hours ago
Next Post
Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.