• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne asusun ba da lamuni na duniya IMF ya sake yin kwaskwarima ga hasashen bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin a shekarar 2024, lamarin dake nuni da cewa tattalin arzikin kasar Sin na iya zarce hasashen da aka yi a baya, duba ga irin gudummawar da ta bayar wajen bunkasar tattalin arzikin duniya a shekarar 2023, wanda ya haura kashi 30 cikin 100, lamarin da ya kara tabbatar da matsayinta ta babbar kasuwa dake bunkasa tattalin arzikin duniya. Wannan kyakkyawar hangen nesa ba wai kawai yana da fa’ida ga kasar Sin ba, har ma zai yi tasiri ga ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, musamman ma kasashe masu tasowa.

Kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa a fannin masana’antu da samar da kayayyaki a duniya. Ta zama cibiyar masana’antu ta duniya, yayin da take jawo hannun jari kai tsaye daga ketare tare da yin amfani da wadatar kwadago mai rahusa da inganci, da inganta ababen more rayuwa, da kwararrun ma’aikata. Kazalika, kwararrun masana’antu na musamman na kasar Sin da ingantattun tsarin samar da kayayyaki sun sa ta zama muhimmin bangare a yawancin masana’antun duniya.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Wasu Ka’idojin Kula Da Muhalli Dake Mayar Da Hankali Kan Yankuna Daban-daban

Kamfanonin kasar Sin na amfani da sabbin dabarun aiki da hidimomi, tare da habaka karfinsu na sarrafa hajoji da hidimomi, da takara mai tsafta, suna zuba jari a kasuwannin kasashen waje. Kuma suna da fa’ida sosai a fannonin da suka hada da fasahohin zamani, da samar da hajoji mara gurbata muhalli, da kuma sauya akalar hada-hadar kasuwanci zuwa dijital. Sun cimma wannan nasarar ne ta hanyar zuba jari a ayyukan kirkire-kirkire a fannonin da suka hada da fasahar 5G, da kirkirarriyar basira (AI), da makamashin da ake sabuntawa, da kuma motocin lantarki wadanda suka jawo hankalin duniya.

A matsayinta na kasar da ta fi fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje, kasar Sin ta kulla huldar kasuwanci mai yawa da kasashen duniya. Alal misali, ayyukanta a karkashin shirin shawarar “ziri daya da hanya daya” (BRI) suna habaka hadin gwiwa da karfafa dangantakar tattalin arziki da kasashe abokan huldarta. Wannan matsayi bisa manyan tsare-tsare ya baiwa kasar Sin damar taka muhimmiyar rawa wajen tsara yanayin cinikayyar duniya da inganta hadin gwiwar tattalin arziki.

Rawar gani da kasar Sin ke takawa a kasuwar duniya ya taimaka dunkule tattalin arzikin duniya. Duniya na tasirantuwa da ci gabanta kamar yadda take ba da kuzari da kwanciyar hankali ga tattalin arzikin duniya, yayin da take more damar samun ci gaba tare da sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Kwato Gidaje 324 Na ‘Yan Fansho Da Aka Karkatar A Jihar Kano

Next Post

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

14 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

15 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

17 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

17 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

19 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

20 hours ago
Next Post
Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.