• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasuwar Sin Na Taimaka Dunkule Tattalin Arzikin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya ne asusun ba da lamuni na duniya IMF ya sake yin kwaskwarima ga hasashen bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin a shekarar 2024, lamarin dake nuni da cewa tattalin arzikin kasar Sin na iya zarce hasashen da aka yi a baya, duba ga irin gudummawar da ta bayar wajen bunkasar tattalin arzikin duniya a shekarar 2023, wanda ya haura kashi 30 cikin 100, lamarin da ya kara tabbatar da matsayinta ta babbar kasuwa dake bunkasa tattalin arzikin duniya. Wannan kyakkyawar hangen nesa ba wai kawai yana da fa’ida ga kasar Sin ba, har ma zai yi tasiri ga ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya, musamman ma kasashe masu tasowa.

Kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa a fannin masana’antu da samar da kayayyaki a duniya. Ta zama cibiyar masana’antu ta duniya, yayin da take jawo hannun jari kai tsaye daga ketare tare da yin amfani da wadatar kwadago mai rahusa da inganci, da inganta ababen more rayuwa, da kwararrun ma’aikata. Kazalika, kwararrun masana’antu na musamman na kasar Sin da ingantattun tsarin samar da kayayyaki sun sa ta zama muhimmin bangare a yawancin masana’antun duniya.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Kasar Sin Ta Fitar Da Wasu Ka’idojin Kula Da Muhalli Dake Mayar Da Hankali Kan Yankuna Daban-daban

Kamfanonin kasar Sin na amfani da sabbin dabarun aiki da hidimomi, tare da habaka karfinsu na sarrafa hajoji da hidimomi, da takara mai tsafta, suna zuba jari a kasuwannin kasashen waje. Kuma suna da fa’ida sosai a fannonin da suka hada da fasahohin zamani, da samar da hajoji mara gurbata muhalli, da kuma sauya akalar hada-hadar kasuwanci zuwa dijital. Sun cimma wannan nasarar ne ta hanyar zuba jari a ayyukan kirkire-kirkire a fannonin da suka hada da fasahar 5G, da kirkirarriyar basira (AI), da makamashin da ake sabuntawa, da kuma motocin lantarki wadanda suka jawo hankalin duniya.

A matsayinta na kasar da ta fi fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje, kasar Sin ta kulla huldar kasuwanci mai yawa da kasashen duniya. Alal misali, ayyukanta a karkashin shirin shawarar “ziri daya da hanya daya” (BRI) suna habaka hadin gwiwa da karfafa dangantakar tattalin arziki da kasashe abokan huldarta. Wannan matsayi bisa manyan tsare-tsare ya baiwa kasar Sin damar taka muhimmiyar rawa wajen tsara yanayin cinikayyar duniya da inganta hadin gwiwar tattalin arziki.

Rawar gani da kasar Sin ke takawa a kasuwar duniya ya taimaka dunkule tattalin arzikin duniya. Duniya na tasirantuwa da ci gabanta kamar yadda take ba da kuzari da kwanciyar hankali ga tattalin arzikin duniya, yayin da take more damar samun ci gaba tare da sauran kasashen duniya. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Kwato Gidaje 324 Na ‘Yan Fansho Da Aka Karkatar A Jihar Kano

Next Post

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

50 minutes ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

18 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

21 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

22 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

Mabambantan Wayewar Kai Ya Kara Kyautata Duniyarmu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.