• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci kafafen yaɗa labarai da su riƙa yaɗa labaran da ke nuna nasarorin da Nijeriya ta samu a tsarin mulkin dimokiraɗiyya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin bikin cikar Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ) shekaru 70 da kafuwa, wanda aka gudanar a cibiyar Shehu Musa Yar’Adua da ke Abuja.

  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
  • Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Bikin ya kuma haɗa da karramawa da ƙaddamar da wani littafi na tarihin ƙungiyar.

Da yake jawabi a madadin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a matsayin Babban Baƙon Taron, kana kuma a matsayin Jagoran Biki, Ministan ya jaddada kusanci da goyon bayan da Shugaba Tinubu yake da shi ga kafafen yaɗa labarai a ƙasar nan.

Ya ce: “Tun daga lokacin da ya kasance cikin masu gwagwarmayar tabbatar da zaɓen 12 ga Yuni tare da jarumai daga cikin ‘yan jarida, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa dangantaka mai ƙarfi da kafafen yaɗa labarai wanda ba a taɓa ganin makamancin sa a tarihin shugabannin Nijeriya ba.”

Labarai Masu Nasaba

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Ya nemi ‘yan jarida da su riƙa amfani da kafafen su wajen haska labarai da ke nuna sauye-sauyen da aka samu a hukumomi, yadda jama’a ke shiga cikin harkokin gwamnati, cigaban ababen more rayuwa da bunƙasar tattalin arziki, a matsayin wani ɓangare na rawar da kafafen ke takawa wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya.

“Yayin da muke bikin shekaru 26 na ci gaba da mulkin dimokiraɗiyya a Nijeriya, dole ne kafafen yaɗa labarai su riƙa yaɗa labaran da ke bayyana nasarorin da dimokiraɗiyyar ƙasar nan ta samu, irin su gyaran hukumomi, gina ababen more rayuwa, shiga jama’a cikin harkokin gwamnati, da kuma cigaban tattalin arziki,” inji shi.

Idris ya ƙara da cewa yayin da kafafen yaɗa labarai suke haska waɗannan nasarori ta hanya mai ma’ana, hakan zai taimaka wajen girmama sadaukarwar da ta haifar da dimokiraɗiyyar Nijeriya tare da ƙarfafa haɗin kan ƙasa da amincewar jama’a da gwamnati.

Ya ƙara da cewa, “Ta yin hakan, kafafen yaɗa labarai suna tabbatar da matsayin su a matsayin ginshiƙi wajen ɗorewa da ƙarfafa tafarkin dimokiraɗiyyar Nijeriya.”

Ya kuma sake tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu tana da cikakken niyyar kare ‘yancin faɗar albarkacin baki da ‘yancin kafafen yaɗa labarai.

“Na sha faɗa a wurare da dama, kuma zan sake faɗa a nan, cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da kare ‘yancin kafafen yaɗa labarai a matsayin ginshiƙi kuma tushen dimokiraɗiyyar Nijeriya.

“Za mu ci gaba da ƙarfafa manufofi da shirye-shiryen da za su ba kafafen damar bunƙasa wajen cika nauyin da ya rataya a wuyan su ga dimokiraɗiyya da al’umma,” inji shi.

Ya kuma taɓo ƙalubalen da ‘yan jarida suke fuskanta a wannan zamani na dijital, ciki har da tasirin Ƙirƙirarrar Basira (AI), yaɗuwar labaran ƙarya da rawar da jaridar jama’a ke takawa.

“Bayyanar Ƙirƙirarrar Basira (generative AI) cikin ‘yan shekarun nan ta ƙara dagula lamarin, inda ake cika mu da hotuna da bidiyo na bogi da yaɗa labaran ƙarya, wanda ya sa aikin jarida na gaskiya ya fi wuya, amma kuma ya fi zama wajibi fiye da da,” inji shi.

Ministan ya bayyana cewa ana nan ana aiki tare da UNESCO domin kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai (MIL) ta musamman a Abuja.

“Shi ya sa muke haɗa gwiwa da UNESCO wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai (MIL) a nan Abuja, wacce za ta zama ta farko irin ta a duniya. Da zarar ta fara aiki, wannan cibiyar za ta zama wani babban tushe wajen inganta aikin jarida na gaskiya a Nijeriya,” inji shi.

Idris ya kuma bayyana shirye-shiryen gwamnatin Tinubu na haɗa kai da NUJ wajen fuskantar muhimman matsalolin aikin jarida da suka haɗa da walwalar ma’aikata, daidaiton jinsi, da sauya fasalin aiki zuwa tsarin zamani.

“Muna da niyyar aiki tare da ku da kuma tallafa maku wajen fuskantar waɗannan matsaloli yayin da kuke ƙoƙarin daidaita kan ku da sabon yanayin ƙarni na 21,” inji shi.

Yayin da ya bayyana cewa ɗaya daga cikin manyan ayyukan kafafen yaɗa labarai shi ne sa ido kan ayyukan gwamnati, Ministan ya buƙace su da su riƙa kallon gwamnati a matsayin abokiyar aiki wajen gina Nijeriya mai zaman lafiya da cigaba.

“Ko da yake kuna da rawar da kuke takawa wajen sa ido a kan gwamnati – kuma muna maraba da hakan – akwai buƙatar ku riƙa kallon mu a matsayin abokan aiki, kuma masu haɗa kai wajen samar da zaman lafiya, tsaro da cigaba da ƙasar nan ke nema ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu,” inji ministan.

Ya kuma taya NUJ murna kan cikar ta shekaru 70 da kafuwa tare da yaba wa ƙungiyar kan ƙaddamar da wani littafi da ke bayyana tarihin ta.

“Ina da yaƙinin cewa aikin jarida yana da buƙatar ko yaushe ya riƙa bayyana labaran sa da kan sa da kuma tsara yadda za a bayyana shi; domin ba wani zai yi mana hakan ba,” inji shi.

Idris ya kuma yaba da girmamawa ga Shugaban Taron, Cif Aremu Olusegun Osoba, da kuma Mamallakin jaridar Vanguard, Mista Sam Amuka-Pemu, bisa gagarumar gudunmawar da suka bayar a harkar jarida da hidima ga jama’a, yana mai cewa su ne abin koyi a wannan sana’ar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

Next Post

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Related

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

53 minutes ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

2 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

3 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

6 hours ago
Borno
Labarai

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

8 hours ago
Yajin aiki
Labarai

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

9 hours ago
Next Post
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra'ila?

LABARAI MASU NASABA

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.