• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ci gaba da kiraye-kiraye ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kan ya cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Uamar Ganduje tare da yawo tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

Wannan lamari ya yi tsamari ne lokacin da matasan jam’iyyar APC na Jihar Kano suka bukaci Tinubu ya tabbatar ya janyo Kwankwaso a cikin jam’iyyar APC muddin yana so ya samu gagarimin goyon bayan al’ummar Kano a zabe mai zuwa.

  • Kyan Alkawari Cikawa
  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Matasan sun yi kira da a cire Ganduje ne daga kan mukamin shugaban jam’iyyar APC sakamakon gazawar da ya yi wajen samun nasara a zaben Gwamnan Jihar Kano.

Matasan sun yi wannan kira ne a Jihar Kano lokacin wani taron manema labarai karkashin jagorancin Ali Mai Sango, inda ya bayyana cewa dawo da Kwankwaso cikin APC zai kara wa jam’iyyar tagomashi a Jihar Kano da zai iya tabbatar da cewa an samu nasara a 2027.

A cewarsa, Kwankwaso ya san duk wata lago na siyasar Kano da ma Arewacin Nijeriya gaba daya wanda zai iya tabbatar da cewa Tinubu ya samu nasarar sake lashe zaben shugaban kasa a karo na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya yi ikirarin cewa Ganduje ya rasa alkiblar siyasarsa a Jihar Kano, amma idan har Kwankwaso ya dawo APC, zai daga kimar jam’iyyar zuwa wani mataki na gaba a zabe mai zuwa.

Kar Ka Dauki Wannan Shawara – Dattawan APC Na Kano

Sai dai kuma dattawan jam’iyyar APC a Jihar Kano sun siffanta kungiyar da ke kiraye-kirayen cire shugaban na jam’iyyar APC, Abdullahi Umar Ganduje a matsayin haramtaccen kungiya da ‘yan adawa suka kafa a jihar.

Dattawan sun bayyana cewa wannan haramtacciyar kungiya ce wanda aka kafa ta domin farfagandar siyasa mai makon mayar da hankali kan abun da ya dace, amma sun fake da kiraye-kiraye sai an cire shugaban jam’iyyar APC wanda ya shafe shekara 5 yana gwagwarmaya kan samuwar wannan gwamnati.

A cikin sanarwar da kungiyar dattawan APC na Kano suka fitar da ke dauke da sa hannun Abubakar Indabawa da Musaddik Wada Waziri bayan ganawa ta musamman, ta bukaci Shugaba Tinubu da daukacin ‘yan Nijeriya da su yi watsi da kiraye-kiraye duk wasu matasa da suke kiran a sauke Ganduje.

A cewar dattawan, a bayyana yake cewa ‘yan adawa ne suka dauki nauyin wadannan matasa domin raba kawunan mambobin jam’iyyar APC ta hanyar yin kira da a cire shugaban jam’iyyar na kasa.

Sun kara da cewa suna kiran kansu matasan APC amma ba a san su ba a jam’iyyar, kawai an dauki nauyinsu ne domin kawo radani a APC, sai dai kuma ba za su yi nasara ba.

Sun ce, “An dai dauki nauyin wadannan matasa ne domin kawo rudani a APC na yin kiraye-kiraye na sai an cire shugaban jam’iyyar wanda ya samu nasarar sasanta fusatattun ‘ya’yan jam’iyyar a wasu jihohi kamar irinsu Ondo da Ribas tun lokacin da ya amshi jagoranci na tsawon wata 7.”

Dattawan sun ce wadannan matasa suna makiyan Ganduje ne saboda sun ga cewa shi kadai ne daga tsofaffin gwamnonin Arewa da ya bai wa Shugaba Tinubu kuri’u mafi rinjaye a zaben shugaban kasa a 2023.

Idan za a iya tunawa dai an fitar da wani rahoto mai cewa Shugaban kasa Tinubu ya bukaci Ganduje ya shirya da Kwankwaso da dukkan mutanen da suke shirin shiga APC.

An dai ta yada wannan rahoton ne bayan da shugaban kasa ya kammala tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano bayan da kotun koli ta zartar da hukuncin tabbatar da zaben Abba Kabir Yusuf a matsayin halartaccen gwamnan Jihar Kano.

Shugaban kasan ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki na Jihar Kano su kai zuciya nesa tare da tattaunawa da mutanen da suke shirin shiga jam’iyyar APC, domin samun hadin kai da kuma ci gaba jihar.

A yayin da wasu suke ganin cewa rahoton kiran da shugaban kasa ya yi wa Ganduje na sasantawa da Kwankwaso ba shi da tushe ballantana makama.

Yanzu haka dai mutane da dama sun zura na mujiya su ga ko dai Kwankwaso zai dawo APC ko kuma zai ci gaba da zama dan jam’iyyar adawa, lokaci ne kadai zai tabbatar da hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

Next Post

‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Kashe ‘Yan Sanda 2 A Katsina

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

'Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Kashe 'Yan Sanda 2 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.