• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Cocin Katolika na Sakkwato, Mathiew Kukah ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya samar da tabbataccen mataki mai dorewa na kawo karshen kashe-kashen al’umma da ya zama ruwan dare, inda ya ce, “Ubangiji ba zai yafe masa ba idan ya kasa sauke nauyin da ke kan sa”.

Kukah a sakonsa na bikin Kirismeti da ya raba wa manema labarai a ranar Litinin, ya bayyana cewa, Shugaban Kasa Tinubu, a matsayinsa na jagora, ya dace ya yi amfani da kwarewa da gogewarsa wajen kawo karshen rikice-rikicen da suka addabi al’ummar kasa na daga bambancin addini, kabilanci ko na yanki.

  • Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB
  • Wadanda Suka Jikkata Yayin Girgizar Kasa A Kasar Sin Sun Samu Kulawar Da Ta Dace

Ya kuma yi magana kan zaben 2023 da sakamakon da ya biyo baya tare da kira ga shugabanni da su dauki matakin daidaita al’amurra a cikin matakin gaggawa. Ya ce shekaru kadan da suka gabata tamkar gwaji ne kan hadin kan kasa da dorewarta.

“Mai girma Shugaban Kasa, a yanzu ka samu abin da ka nema kuma kake mafalki, wanda ka jima ka na muradi. A sama da shekaru 20 ka daura damarar zama Shugaban Kasa, ka yi yekuwar neman zaben kafa sabuwar Nijeriya ta hanyar canza fasalin kasa, a tsawon shekaru, ka yi gwagwarmayar kafa Dimokuradiyya ta hanyar yaki da mulkin soji, don haka a yanzu lokaci ya yi da za ka kawo karshen matsalolin al’umma.

“A yanzu kai ne matuki a gidan gaba, a karkashin ikonka, wajibi ne Nijeriya ta dawo saman turba, a bisa ga jagorancinka, ya zama dole mu kawo karshen rikice-rikicen addini, kabilanci da na yanki. Ka samu cikakken lokacin tunanin amsa tambayoyin al’umma wadanda ke kukan samun amsa. A yanzu makomar ka da ta ‘yan kasa ta na a hannunka.” In ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Kukah ya bayyana cewar Tinubu ba ya da kowane irin uzuri a wajen ubangiji ko ga al’umma, ya ce ubangiji ko tarihi ba za su taba yi masa afuwa ba idan ya kasa sauke nauyi, don haka, a yanzu dukkanin idanu da kunnuwa suna a kansa.

Kukah ya kara da cewa, suna yi masa addu’ar samun kasa mai cike da hadin kai.

“Mun ga wasu matakan farko na tsare-tsare wadanda suka haifar da rudani, fargaba da yabo wanda abin da aka yi tsammani ne. Muna fatan ganin alkawalin sauyi da ka yi mana.” Kukah ya bayyana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bukukuwan KirismetiKukahYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ware Biliyan 1.3 Don Zamanantar Da Kafafen Yaɗa Labaran Jihar

Next Post

An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

24 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 days ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

3 days ago
Next Post
An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.