• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma

by Sulaiman and Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Kukah

Shugaban Cocin Katolika na Sakkwato, Mathiew Kukah ya bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya samar da tabbataccen mataki mai dorewa na kawo karshen kashe-kashen al’umma da ya zama ruwan dare, inda ya ce, “Ubangiji ba zai yafe masa ba idan ya kasa sauke nauyin da ke kan sa”.

Kukah a sakonsa na bikin Kirismeti da ya raba wa manema labarai a ranar Litinin, ya bayyana cewa, Shugaban Kasa Tinubu, a matsayinsa na jagora, ya dace ya yi amfani da kwarewa da gogewarsa wajen kawo karshen rikice-rikicen da suka addabi al’ummar kasa na daga bambancin addini, kabilanci ko na yanki.

  • Na Yi Iya Bakin Ƙokarina Lokacin Da Nake Riƙe Da Shugabancin Nijeriya — IBB
  • Wadanda Suka Jikkata Yayin Girgizar Kasa A Kasar Sin Sun Samu Kulawar Da Ta Dace

Ya kuma yi magana kan zaben 2023 da sakamakon da ya biyo baya tare da kira ga shugabanni da su dauki matakin daidaita al’amurra a cikin matakin gaggawa. Ya ce shekaru kadan da suka gabata tamkar gwaji ne kan hadin kan kasa da dorewarta.

“Mai girma Shugaban Kasa, a yanzu ka samu abin da ka nema kuma kake mafalki, wanda ka jima ka na muradi. A sama da shekaru 20 ka daura damarar zama Shugaban Kasa, ka yi yekuwar neman zaben kafa sabuwar Nijeriya ta hanyar canza fasalin kasa, a tsawon shekaru, ka yi gwagwarmayar kafa Dimokuradiyya ta hanyar yaki da mulkin soji, don haka a yanzu lokaci ya yi da za ka kawo karshen matsalolin al’umma.

“A yanzu kai ne matuki a gidan gaba, a karkashin ikonka, wajibi ne Nijeriya ta dawo saman turba, a bisa ga jagorancinka, ya zama dole mu kawo karshen rikice-rikicen addini, kabilanci da na yanki. Ka samu cikakken lokacin tunanin amsa tambayoyin al’umma wadanda ke kukan samun amsa. A yanzu makomar ka da ta ‘yan kasa ta na a hannunka.” In ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Kukah ya bayyana cewar Tinubu ba ya da kowane irin uzuri a wajen ubangiji ko ga al’umma, ya ce ubangiji ko tarihi ba za su taba yi masa afuwa ba idan ya kasa sauke nauyi, don haka, a yanzu dukkanin idanu da kunnuwa suna a kansa.

Kukah ya kara da cewa, suna yi masa addu’ar samun kasa mai cike da hadin kai.

“Mun ga wasu matakan farko na tsare-tsare wadanda suka haifar da rudani, fargaba da yabo wanda abin da aka yi tsammani ne. Muna fatan ganin alkawalin sauyi da ka yi mana.” Kukah ya bayyana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

An Wallafa Littafin Xi Jinping Game Da BRI Bugun Shekarar 2023

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Kukah

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025
Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taɓa Yi (2)

October 10, 2025
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

October 10, 2025
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.