• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Kirismeti: Shugaban Karamar Hukumar Soba Ya Tallafa Wa Kiristoci Da Buhunan Shinkafa Fiye Da 500
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kiristoci ta Nijeriya, CAN ta yabawa shugaban karamar hukumar Soba, Hon. Muhammad Lawal Shehu, bisa gudunmawar shinkafar da ya bai wa mambobinsu a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

 

Shugaban CAN na Soba, Fasto Nazaral Daniel John wanda ya bayyana godiyarsa bayan karbar kyaututtukan a sakatariyar Dahiru Maigana, inda ya bayyana cewa, Hon. Shehu shi ne shugaba na farko da ya yi irin wannan gagarumin tallafin wanda ya farantawa rayuwar daruruwan mabiya addinin Kirista a cikin kasa da watanni uku a kan kujerar mulki.

  • Sin Ta Gabatar Da Rukuni 2 Na Kayayyakin Agajin Gaggawa Ga Al’ummun Gaza Ta Mashigin Kasar Masar
  • Mutum 2 Sun Mutu Yayin Da ‘Yansanda Suka Ceto Mutum 10 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

Yayin da yake fatan samun makoma mai haske a karkashin jagorancinsa, Fasto John ya yi addu’ar Allah ya saka masa da mafificin alheri a gwamnatinsa.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

“A madadin CAN, karamar hukumar Soba, muna so mu mika godiyarmu bisa irin kyautar da kuka yi mana na Kirsimeti da kuma sanya farin ciki a fuskokinmu, mun gode, Allah Madaukakin Sarki Ya saka muku da alheri. Muna alfahari da kasancewar ku jagoranmu.” , in ji Fasto John.

Soba

A yayin bikin kaddamar da rabon shinkafar, Shugaban karamar hukumar, Hon. Muhammad Lawal Shehu ya bayyana cewa wannan karimcin ya yi daidai da manufofin Gwamna Uba Sani na inganta jin dadin rayuwar al’umma.

 

Hon. Shehu, wanda ya samu wakilcin Mataimakinsa Hon. Muhammad Garba Baban-baba, ya bayyana cewa an raba sama da buhunan shinkafa 500, kowanne mai nauyin kilo 10, ga Kiristoci, domin taimaka musu wajen murnar bukukuwan Kirsimeti da na karshen shekara.

Soba

Baban-baba ya nemi goyon bayan al’ummomin yankin domin cimma burin gwamnati na inganta karamar hukumar Soba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Masu Shiga Wasannin Kankara A Sin Ya Kai Miliyan 313 Tun Bayan Gasar Olympics Ta Hunturu Ta Beijing

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

2 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

2 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

4 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

5 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

8 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

9 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda Da Dama Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Katsina

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.