• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Gillar Sojoji 17: Tinubu Ya Shafa Wa Idonsa Toka, Sojoji Sun Kai Mamaya

by Bello Hamza and Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Kisan Gillar Sojoji 17: Tinubu Ya Shafa Wa Idonsa Toka, Sojoji Sun Kai Mamaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

A halin yanzu tsoro da tashin hankali ya kama al’umma Jihar Bayelsa yayin da ma’aikatar tsaro da zafafa bincike don gano wadanda suka kashe sojoji 17 a garin Okuoma da ke karamar hukumar Ughelli ta Kudu ta Jihar Delta.

Lamarin ya kara tayar da hankulan mutanen jihar ne ganin cewa, babban wanda ake zargi da jagorantar kisan sojojin wani ne da yake da alaka na kusa da wasu jami’an gwamnati.

  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Zargin Blinken Wai Sin Na Gurbata Yanayin Sadarwar Duniya
  • MTC Da Huawei Sun Gudanar Da Gwajin 5G Na Farko A Hukumance A Namibia

Tuni dai kisan sojojin ya haifar da rashin jituwa tsakanin Gwamna Douye Diri da wanda ya gada kuma tsohon ministan albarkatun man fetur, Cif Timipre Sylba. Gwamna Diri ya zargi Cif Sylba da kokarin siyasantar da kisan da aka yi wa sojojin.

A binciken da LEADERSHIP Hausa ta yi ta gano cewa, hedikwatar tsaro ta takaita bincikenta ne a kan kisan zuwa kan babban wanda ake zargi da jagorantar kisan wanda kuma shi ne shugaban matasa na kabilar Okuoma (Mun sakaya sunansa). Hankali ya tashi kwarai da gaske a kan kisan da aka yi wa Kwamandan sojojin Bataliya na 181 da ke aiki a karamar hukumar Bomadi ta jihar Delta, Laftanar Kanal A. H. Aliu,

sauran hafsoshin da aka kashe a kwantan baunar da matasan suka yi wa sojojin sun hada da Manjo S.D. Shafa, Manjo D.E. Obi da kuma Kaftin U. Zakari.

Bayani ya nuna cewa, a ranar Lahadi ne fusatattun sojoji suka mamaye yankin kabilar Ijaw da ke Jihar Bayelsa, bayanai sun nuna cewa, wanda ake zargin mahaifiyarsa ta fito ce daga garin Igbomotoru, da ke karamar hukumar Ijaw ta Kudu amma kuma ba a samu sa’ar kama shi ba.

Bincike ya nuna cewa, wanda ake zargin ya tsallake ne bayan da ya samu bayanan sirri na zuwan sojojin amma kuma mamayar da sojojin suka yi ya haifar da barnar rayuka da dukiya mai yawa. An kiyasta mutuwar akalla mutum 11 a mamayar da sojojin suka kai.

LEADERSHIP ta kuma gano cewa, dangantakar da ke tsakanin babban wanda ake zargin da wasu jami’an gwamnati ya sa masu ruwa da tsaki a jihar zargin cewa, lallai akwai yiwuwar jami’an gwamnati ke boye shi daga shiga hannun hukuma zuwa wannan lokacin. Wanda ake zargin yana daga cikin manyan wadanda suka tsayu wajen ganin an sake zabar Gwamna Douye Diri a zaben gwamna da aka yi a shekarar da ta gabata.

A kan haka wata majiya ta bayyana wa LEADERSHIP cewa, a halin yanzu, jami’an tsaron sun karkata ne wajen neman iyalai da abokan siyasan wanda ake zargin a fadin jihar.

A bisa wannan tsarin ne, jami’an tsaro suka sanya ido na musamman a kan shugaban karamar hukumar Ijawa ta Kudu, Mr. Lucky Okodeh, wanda dan’uwa ne ga wanda ake zargin shi ne jagoran matasan da suka kashe sojojin. Haka kuma wani aminin wanda ake zargin wanda shugaba ne na wani babban kwamiti a jihar yana cikin wadanda aka sa wa ido na musamman don ganin an cafko babban wanda ake zargi da kisan. Jami’an staro sun sa ido a kan wadanna jami’an gwamnatin ne don ganin ko za su samu bayanai da zai taimaka musu kaiwa ga kama wanda ake zargi da jagorantar kisan sojojin.

A halin yanzu kuma wata kungiyar ‘yan kabilar Urhobo mai suna ‘Urhobo Renaissance Assembly’ ta nuna bacin ranta a kan yadda jami’an tsaro suke kai harin mamaya a yankuna kabilar Urhobo tun bayan da aka kashe sojoji a garin Okuama.

A halin da ake ciki kuma, a matsayinsa na babban kwamandan askarawan Nijeriya, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya shafa wa idonsa toka inda ya umarci daukar matakin ba-sani-ba-sabo a kan wadanda suka kashe sojoji 17 a Jihar Delta.

Tinubu ya bayyana cewa duk wani farmaki da aka kai wa sojojin tamkar ayyana yaki ne kan Nijeriya. Ya ce ko kadan ba za a lamunci irin wannan mummumar aika-aika ba.

Shugaba Tinubu ya yi wannan gargadi ne a cikin wata sanarwa da ke dauke da sa hannunsa a farkon makon nan. Inda ya bai wa sojoji cikakken ikon tabbatar da tsaro tare da bankado wadanda ake zargi da aikata laifin domin gurfanar da su a gaban kuliya.

Shugaban kasan ya siffanta kisan a matsayin abin da ba za a lamunta ba, sannan ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa hafsoshin tsaro za su yi duk mai yuwuwa wajen daukan matakan da suka dace kan wannan mummuman lamari.

A yanzu haka dai an jibge sojoji a yankin Okuama da ke cikin karamar hukumar Ughelli ta kudu a Jihar Delta, domin bankado maharan da suka kashe sojoji masu wanzar da zaman lafiya a yankin.

Sojojin dai rike da muggan makamai a kokarinsu na binciko masu laifin a yankin sun banka wuta a wasu gine-gine da ake kyautata zato maboyar wadanda ake zargin ne.

Bisa amfani da cikakken ikon da Shugaba Tinubu ya bayar kan kisan sojojin, shalkwatar tsaro ta bayyana cewa ‘yan farfaganda sun yi kadan su hana su cika aika. Sannan ta sanar da daukan matakin gaggawa kan wadanda suka kashe sojoji a yankin Okuama na Jihar Delta.

Daraktan yada labarai na shalkwatar tsaron, Manjo Janar Edward Buba ya bayyana hakan a cikin wata nasarwa da ya fitar.

Su ma Ministocin tsaro, Badaru Abubakar da Bello Matawalle, sun yi tir da wannan kisan, suka ce gwamnatin tarayya ba za ta lamunci duk wata barazana ga tsaron kasar nan ba.

A nashi bangaren, Babban hafson sojoji, Laftanan Janar, Taoreed Lagbaja, ya bayyana cewa babu wajen buya ga wadanda suka kashe sojojin.

A cikin sanarwar da shalkwatar tsaron ta fitar ta ce, “Rundunar sojin Nijeriya tana tabbatar da cewa za ta dauki matakan da suka dace na ganin an damke tare da hukunta wadanda suka yi wannan kisan.

“Duk da haka, rundunar sojin Nijeriya za ta kasance mai bin doka da kuma mutunta hakkin Dan’adam wajen daukar mataki. Ba za mu taba barin fushinmu ya kai ga karya doka ba,” in ji shalkwatar tsaro.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Nuryan Maimaiti Ke Bayyana Labarai Kan Kogunan Dubban Buddha Na Kezil

Next Post

Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…

Related

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

4 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

5 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

8 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

9 hours ago
Next Post
Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…

Yawaitar Hare-haren ' Yan Bindiga A Jihar Kaduna…

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.