• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Masu Mauludi A Kaduna Abun Takaici Ne – Bukola Saraki

byAbba Ibrahim Wada
2 years ago
Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki yayi Allah-wadai da kashe mutane masu Maulidi bisa kuskure a kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna. 

Wannan na cikin wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan kafafen yada labarai, Abba Ibrahim Wada ya fitar.

  • Dan Kwallo Ya Mutu Ana Tsaka Da Atisaye A Ogun
  • Kaduna: Muna Neman Afuwar Kisan Masu Maulidi – Hafsan Sojin Kasa

Saraki, ya ce ya zama dole a yi bincike domin gano wadanda suka aikata wannan abu sannan a dauki matakin hana faruwar irin hakan a nan gaba.

“Kashe mutane ta hanyar harba musu bom da aka yi a lokacin da suke bikin Mauludi a kauyen Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna abin takaici ne.

“Da ni da iyalina muna mika sakon ta’aziyyarmu ga al’umma da gwamnatin Jihar Kaduna da iyalan wadanda wannan ibtila’i ya fadawa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

“Ina addu’ar Allah Ya jikan wadanda suka rasu sannan wadanda suka samu rauni kuma Allah Ya ba su lafiya.

“Sai dai bayan wannan mummunan ibtila’i, ya zama dole mu gujewa faruwar irin wannan a nan gaba. Sannan akwai bukatar a gudanar da bincike domin a gano yadda wannan abin ya faru sannan a kawo hanyoyin gujewa faruwar hakan a nan gaba.

“Har ila yau, ya zama dole a sake nazari, wannan ya zama izina, bugu da kari a hada hannu waje guda wajen sake gina kishin kasa a zukatan mutane, adalci da kaunar juna domin tabbatar da kiyaye lafiyar duk wani dan kasa,” in ji Saraki.

A ranar Lahadin da ta gabata ne jirgin sojin Nijeriya ya jefa wa wasu mutane da ke gudanar da taron Mauludi bom, lamarin da ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 85 da kuma jikkata da dama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

‘Yansandan Sun Kama Masu Laifi 130 A Watan Nuwamba A Katsina

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version