• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi, sun samu nasarar cafke wani matashi dan shekara 35 a duniya, Mustapha Tahiti, jami’in da ke aikin tattara bayanai a asibitin kula da lamuran haihuwa da ke Kofar Ran a cikin garin Bauchi bisa yunkurinsa na kashe dan uwansa da matarsa ta hanyar dambara musu allurar da zai kashe su. 

‘Yansanda sun ce, Tahiri ya shiga hannu ne a ranar 6 ga watan Maris din 2024 biyo bayan rahoton sirri da ya shigo hannun sashin kula da manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi (CID).

  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna
  • Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

A sanarwar manema labarai Sufuritandan dan-sanda, Ahmed Mohammed Wakil, ya fitar a ranar Alhamis tare da aiko da kwafinta wa jaridar LEADERSHIP, ta ce, cikin gaggawa bayan samun rahoton faruwar lamarin jami’an suka hanzarta inda suka tasa keyar wanda ake zargi a lokacin da ke tsaka da kokarin aiwatar da shirinsa.

“A lokacin da ke fuskantar tambayoyi, wanda ake zargin ya amince da aikata laifinsa kuma ya shaida cewar ya zuba sinadarin kashe kwari a cikin sirinji da nufin yin amfani da karfin tsiya wajen damfara wa Ma’auratan domin su mutu,” Wakil ya shaida.

Sanarwar ta kuma zargi Tahiti da cewa yana da shirin zai yi awun gaba da muhimman kayayyaki da kadarorin ma’auratan bayan sun mutu, idan ya samu nasarar kan aniyarsa.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

“Ya kuma ce zai kwashe muhimman kayayyakinsu idan ya kashe dukkaninsu dan uwansa da matarsa.”

‘Yansandan suka ce sun kwato sirinjin da wanda ake zargin yake kokarin amfani da shi wajen kashe mata da mijin bayan ya dura sinadarin da ka iya kashe su kai tsaye.

Binciken ‘yansanda ya kuma gano cewa, wanda ake zargin na tsananin gaba da jin haushin wanda ya yi kokarin kashewa bisa dalilin cewa ya auri matar babban dan uwansa da ya rasu, wacce shi din yake matukar so da nufin aurenta, amma matar ta ce ba ta son aurensa.

Tahiti ya sha gargadin wanda lamarin ya shafa da cewa kada ya kuskura ya auri bazawarar amma ya ki saurare ya je ya aure ta.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Auwal Musa Mohammed ya umarci a gudanar da wanda ake zargi a gaban kuliya mance sabo da zarar aka kammala gudanar da bincike.

Kwamishinan ya bai wa al’umman jihar tabbacin azamarsa da kokarinsa wajen cigaba da yaki da ta’addanci da masu aikata laifuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna

Next Post

Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

7 hours ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

7 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

8 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

9 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

12 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

13 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.