• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Kishi: ‘Yansanda Sun Cafke Ma’aikacin Lafiya Da Yunkurin Hallaka Ma’aurata A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi, sun samu nasarar cafke wani matashi dan shekara 35 a duniya, Mustapha Tahiti, jami’in da ke aikin tattara bayanai a asibitin kula da lamuran haihuwa da ke Kofar Ran a cikin garin Bauchi bisa yunkurinsa na kashe dan uwansa da matarsa ta hanyar dambara musu allurar da zai kashe su. 

‘Yansanda sun ce, Tahiri ya shiga hannu ne a ranar 6 ga watan Maris din 2024 biyo bayan rahoton sirri da ya shigo hannun sashin kula da manyan laifuka ta rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi (CID).

  • Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna
  • Sudan Ce Kasa Mafi Fama Da Yunwa A Afrika – MDD

A sanarwar manema labarai Sufuritandan dan-sanda, Ahmed Mohammed Wakil, ya fitar a ranar Alhamis tare da aiko da kwafinta wa jaridar LEADERSHIP, ta ce, cikin gaggawa bayan samun rahoton faruwar lamarin jami’an suka hanzarta inda suka tasa keyar wanda ake zargi a lokacin da ke tsaka da kokarin aiwatar da shirinsa.

“A lokacin da ke fuskantar tambayoyi, wanda ake zargin ya amince da aikata laifinsa kuma ya shaida cewar ya zuba sinadarin kashe kwari a cikin sirinji da nufin yin amfani da karfin tsiya wajen damfara wa Ma’auratan domin su mutu,” Wakil ya shaida.

Sanarwar ta kuma zargi Tahiti da cewa yana da shirin zai yi awun gaba da muhimman kayayyaki da kadarorin ma’auratan bayan sun mutu, idan ya samu nasarar kan aniyarsa.

Labarai Masu Nasaba

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

“Ya kuma ce zai kwashe muhimman kayayyakinsu idan ya kashe dukkaninsu dan uwansa da matarsa.”

‘Yansandan suka ce sun kwato sirinjin da wanda ake zargin yake kokarin amfani da shi wajen kashe mata da mijin bayan ya dura sinadarin da ka iya kashe su kai tsaye.

Binciken ‘yansanda ya kuma gano cewa, wanda ake zargin na tsananin gaba da jin haushin wanda ya yi kokarin kashewa bisa dalilin cewa ya auri matar babban dan uwansa da ya rasu, wacce shi din yake matukar so da nufin aurenta, amma matar ta ce ba ta son aurensa.

Tahiti ya sha gargadin wanda lamarin ya shafa da cewa kada ya kuskura ya auri bazawarar amma ya ki saurare ya je ya aure ta.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi CP Auwal Musa Mohammed ya umarci a gudanar da wanda ake zargi a gaban kuliya mance sabo da zarar aka kammala gudanar da bincike.

Kwamishinan ya bai wa al’umman jihar tabbacin azamarsa da kokarinsa wajen cigaba da yaki da ta’addanci da masu aikata laifuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bauchi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahara Sun Sace Dalibai 200 A Kauyen Kaduna

Next Post

Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Related

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
Labarai

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

3 hours ago
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
Labarai

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

3 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
Manyan Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

5 hours ago
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
Labarai

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

9 hours ago
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

22 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

1 day ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

Xi Ya Jaddada Zurfafa Gyare-gyare Don Inganta Kwarewa A Sabbin Fannoni

LABARAI MASU NASABA

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

June 15, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

June 15, 2025
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

June 15, 2025
UEFA

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

June 15, 2025
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

June 15, 2025
Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

Wakilin Sin A IAEA Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Sarrafa Nukiliyar Iran

June 14, 2025
Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar

June 14, 2025
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.