Masana da jami’ai a Nijeriya, sun yaba wa ci gaba na a-zo-a-gani da karin kuzarin da ake samu a hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Nijeriya, suna masu bayyana kokarin da aka yi zuwa yanzu a hadin gwiwar bangarorin biyu a tafarkin zamanantar da kansu.
Masanan sun bayyana haka ne yayin taro na biyu na bayan taron FOCAC da aka yi ranar Alhamis a Abuja, babban birnin kasar. Cibiyar nazarin dangantakar Sin da Afrika dake Nijeriya ce ta shirya taron mai taken “Hada Hannu Wajen Zamanantar da Sin da Afrika da cimma shirye-shirye 10 na Hadin Gwiwa a Cikin Al’ummar Sin da Afrika mai Makoma ta Bai Daya a Ko da Yaushe.”
Da yake jawabi, daraktan cibiyar nazarin Sheriff Ghali Ibrahim, ya ce daga Bandung a 1955 zuwa Beijing a 2024, Sin da Afrika sun ci gaba da bijirewa mulkin mallaka da danniya, yayin da Sin ta yi ta goyon bayan kasashen Afrika wajen zamanantar da kansu da samu ci gaba, ta hanyar zuba jari da bayar da tallafi da rance da sauransu.
Masu gabatar da jawabai da dama sun bayyana ci gaban da aka samu a baya-bayan nan a hadin gwiwar Sin da Nijeriya, suna masu jinjinawa hadin gwiwar abota bisa manyan tsare-tsare da shugabannin kasashen biyu suka cimma a bara. Sun kuma bukaci hukumomin Nijeriya su kyautata amfani da manufar soke haraji ta Sin, su kuma yayata damarmakin ci gaba da cimma burikan kasashen biyu na samun karin kuzari. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp