• English
  • Business News
Sunday, September 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano

by Muhammad
2 months ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Manyan Labarai
0
Kotu Ta Kori Ƙarar Da APC Ta Shigar Kan Dakatar Da Kuɗaɗen Ƙananan Hukumomin Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Kano ta yi watsi da ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar, inda ta nemi dakatar da rabon kuɗaɗen da ake bai wa ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano kason su.

Jam’iyar APC, ƙarƙashin shugabanta na jihar, Abdullahi Abbas, ta shigar da ƙarar tun cikin watan Nuwamba 2024, inda ta nemi a soke shugabancin shugabannin ƙananan hukumomi da NNPP ke riƙe da su, bisa hujjar cewa ba su ci zaɓe ta hanyar dimokuraɗiyya ba kamar yadda Sashe na 7(1) na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ya tanada.

  • NNPP Ta Lashe Zaben Kananan Hukumomi A Kano
  • Na Yi Alƙawarin Kawo Wa APC Kano A Zaɓen 2027 – Doguwa

Jam’iyyar ta kuma nemi kotu da ta hana Gwamnatin Tarayya da Babban Bankin Nijeriya (CBN), da Akanta Janar na Ƙasa raba kuɗaɗen zuwa ƙananan hukumomin na Kano.

Masu amsa ƙarar sun haɗa da:

Kwamitin Raba Kuɗaɗen Tarayya (FAAC)

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

 Hukumar Raba Kuɗaɗe da Tsare-Tsare (RMAFC)

 Ministan Kuɗi

Mai binciken Kuɗ na ƙasa

Alƙalin-Alƙalai na Ƙasa

A hukuncin da Alƙali Simon Amobeda, ya yanke a ranar Litinin, ya ce ƙarar ba ta da tushe bare makama. Ya ce bayan kotun ɗaukaka ƙara ta yanke cewa babbar kotun jihar Kano ce kaɗai ke da ikon sauraron irin wannan ƙara, masu ƙara suka nemi janye ƙarar, amma ba su gabatar da takardar janye wa cikin kwanaki 14 da doka ta tanada ba.

Masu amsa ƙarar sun nemi a yi watsi da ƙarar da tara.

Lauyan Alƙalin-Alƙalai na Ƙasa ya buƙaci tarar miliyan 2.5

Lauyan Kano ya buƙaci naira biliyan 2

Lauyan KANSIEC ya buƙaci biyan naira miliyan 2, yana cewa sun sha wahala a shari’ar.

 Lauyan shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 ya nemi  miliyan 44

Alƙali Amobeda ya yanke cewa a yi watsi da ƙarar gaba ɗaya, ba wai a kore ta na ɗan lokaci ba, tare da ƙin bayar da tara ga masu amsa ƙarar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ANPPAPCkanoKotuƘananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ya Hada Sassan Kasa Da Kasa

Next Post

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Related

Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

3 hours ago
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai
Manyan Labarai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

8 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira

18 hours ago
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira
Manyan Labarai

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

1 day ago
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph
Manyan Labarai

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

1 day ago
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

2 days ago
Next Post
Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

Ana Iya Samun Masu Samar Da Kayayyaki Iri-Iri Cikin Awa Daya A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi

Jami’an Tsaro Sun Ceto Fasinjoji 8 Da Aka Sace A Kogi

September 28, 2025
Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

Yaushe Mourinho Zai Koyar Da Kwallon Kafa A Kasashen Jamus Da Faransa?

September 28, 2025
Harin Bam: Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Sake Ginin Garin Tudun Biri 

Gwamnatin Kaduna Za Ta Horas Da Ɗalibai 32,000 Sana’oin Hannu A Duk Shekara – Maiyaki

September 28, 2025
Shari’a: Ganduje Ya Ki Na’am Da Tayin Jakadanci A Kasashen Afirka 

Gwamna Yusuf Ya Samu Kuɗaɗe A Cikin Wata 6 Fiye Da Yadda Na Samu A Cikin Shekaru 8 – Ganduje 

September 28, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Kano

Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano

September 28, 2025
Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

September 28, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

September 28, 2025
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

September 28, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.