• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Kori Dan Majalisar LP, Omolie, Ta Ayyana Elumelu A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Kori Dan Majalisar LP, Omolie, Ta Ayyana Elumelu A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun sauraron kararrakin zaben ‘yan majalisun tarayya da na jiha a jihar Delta, a ranar Litinin ta kori Hon. Ngozi Omolie na jam’iyyar Labour (LP), a matsayin mambar Majalisar wakilai da ke wakiltar mazabar Aniocha/Oshimili a Majalisar wakilai ta tarayya daga jihar Delta.

Baya nan, kotun ta dawo wa tsohon wanda ke kan kujerar, Hon. Ndudi Elumelu na jam’iyyar PDP kujerarsa a matsayin halastaccen wanda ya lashe zaben mamban Majalisar wakilai da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu a wannan mazabar.

  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia
  • Dan Takarar Gwamnan Labour Party Ya Janyewa Binani Takararsa A Jihar Adamawa

Mr Okolie dai ya tumbuke tsohon shugaban marasa rinjaye Ndudi Elumelu ne a zabe ranar 25 ga watan Fabrairu, yayin da shi Elumelu ya kalubanci sakamakon a gaban kotu.

Okolie dai ya samu nasara ne da kuri’u 53, 879 da ya kayar da Elumelu mai kuri’u 33, 466.

Mr Elumelu, ya shigar da korafi ya na kalubalantar ingancin tsayar da Okolie a matsayin dan takara bisa zargin cewa bai cika sharuda da ka’idojin da dokokin zabe suka shimfida ba.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Ya ce, LP ba ta tsayar da Okolie ta hanyar da ya dace ba domin a cewarsa jam’iyyar ta gabatar da sunansa (Okolie) ne kawai a matsayin dan takara amma ba mambar jam’iyyar ba ne.

Kotun mai alkalai uku karkashin jagorancin A.Z. Mussa, wacce ke zamanta a garin Asaba, a hukuncinta ta amince Elumelu ne sahihin wanda ya ci zaben.

Don haka ne kotun ta zartar da hukuncin cewa Elumelu ne zababen dan majalisar mazabar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuLP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Dauki Dukkan Matakan Da Suka Dace Don Kiyaye Tsaron Kasa 

Next Post

Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

19 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

4 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

5 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

17 hours ago
Next Post
Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Bi Ra’ayinta Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.