• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Sake Turawa Rarara Sammaci Kan Taurin Biyan Bashi A Kano

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Sake Turawa Rarara Sammaci Kan Taurin Biyan Bashi A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun shari’ar addinin Musulunci da ke Kano ta bada umarnin sake rubuta wa shahararren mawakin siyasa, Dauda Adamu Kahutu (Rarara) sabuwar takardar sammaci sabida kin mutunta gayyatarta.

 

Jaridar Daily Nigerian Hausa ta rahoto cewa, Kotun, wacce ke zamanta a unguwar Rijiyar Zaki da ke birnin Kano wacce ke karkashin Mai Shari’a Halhalatul Khuza’i Zakariyya, ce ta bayar da umarnin yayin zamanta na ranar Talata.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 1, Sun Harbe Wasu 2 A Kano

Ana karar Rarara ne kan kin biyan wasu kudaden wasu wayoyin salula da yake karba yana raba wa mutane daga hannun wani dan kasuwa mai suna Muhammad Ma’aji.

 

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Yawan kudin dai ya kai kimanin Naira miliyan goma da dubu dari uku.

 

Lauyan mai kara Barista I. Imam ya shaida wa kotun cewa, wanda ake karar bai mutunta sammacin da aka kai masa ba saboda kin halartar zaman kotun.

 

Lauyan ya roki kotun da ta bayar da umarnin a kamo Rarara kasancewar ya raina kotun.

 

Sai dai ya kara da cewa bai san ko sammacin da aka ba wa wanda ake karar ya isa gare shi ba, ko kuma a’a.

 

Kotun ta tambayi jami’inta da ya kai sammacin, Isma’il Zuhudu, ko ya ba Rarara hannu da hannu, inda ya ce ya like masa takardar a kofar gidansa kamar yadda kotun ta yi umarni, sakamakon sun neme shi don ya bavshi hannu da hannu amma bai same shi ba.

 

Mai Shari’a, Halhalatul Khuza’i Zakariyya, ya ce kasancewar wanda ake tuhuma bai zo ba kuma bai aiko ba, kotun ta yi masa uzuri saboda wannan ne karo na farko da ya yi haka.

 

Daga nan ne ya ba da umarnin a sake rubuta sabon sammaci ga Rarara a sake kai masa ko kuma like masa a kofar gidansa da ke kan titin gidan Zoo a Kano tare da wallafa sammacin a shafukan sada zumunta da kafafan yada labarai.

 

Kotun ta kuma sanya ranar Alhamis, 13 ga watan Afrilu, 2023 domin ci gaba da sauraran karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Jihar Filato Za Ta Ci Gaba Da Zama A Garkame – Kwamishinan ‘Yansanda

Next Post

Kasar Sin Dake Kokarin Bude Kofa Da Hadin Kai Da Kasa Da Kasa Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ingiza Bunkasuwa Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

8 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

9 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

12 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

14 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

17 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

18 hours ago
Next Post
Kasar Sin Dake Kokarin Bude Kofa Da Hadin Kai Da Kasa Da Kasa Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ingiza Bunkasuwa Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Kasar Sin Dake Kokarin Bude Kofa Da Hadin Kai Da Kasa Da Kasa Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ingiza Bunkasuwa Da Kwanciyar Hankalin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.