• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

by Abubakar Abba
2 years ago
Goje

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da karar da Sanata Mohammed Danjuma Goje, ya shigar a gabanta na kalubalantar korara da kwamitin jami’yyar APC na mazabar Kashere da ke jihar Gombe ya yi masa.

Kwamitin ya dakatar da Goje ne daga baya kuma ya kore shi daga APC a watan Afrilu, 2023.

  • INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe
  • Masarautar Zazzau Ta Dakatar Da Marafan Yamman Zazzau Kan Daukar Doka A Hannunsa

Kwamitin ya kore shi ne, bisa zargin kin shiga ayyukan gangamin yakin neman zaben APC a dukkan matakai har da na yakin neman zaben shugaban kasa da kuma yi wa ‘yan takarar majalisar dikokin jihar da tarayya zagon kasa a lokacin yankin neman zaben.

Goje ya kuma ki yi wa shugabannin jami’yyar da’a da kuma kin yin biyayya ga mahukuntan da ke jagorantar jam’iyyar a jihar.

An kori Goje daga APC ne, bayan da kwamitin APC na mazabar Kashere ya mika rahotonsa na binciken zargin da ake yi wa Goje.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

A cikin rahoton kwamitin, ya gano cewa, zargin da ake yi wa Goje, ya tabbata, inda kwamitin ya bayar da shawarar a gaggauta dakatar da shi da kuma korarsa daga jam’iyyar.

Shugabancin APC na mazabar Kashere sun amince da rahoton kwamitin binciken, inda kuma babban kwamitin APC na jihar Gombe da sauran kwamitocin kananan hukumomi 11 na jihar, su ma suka amince da rahoton kwamitin da ya dakatar tare da korar Goje daga APC.

Bisa wannan dakatarwar ne da kuma korarsa, hakan ya sa Goje ya garzaya zuwa kotun don kalubalabatar matakin.

Sai dai, a hukuncin da alkalin babbar kotun da ke Abuja wadda mai shari’a alkali Obiora Egwatu ke jagoranta a zaman da ta yi a ranar Talata, ta yi fatali da karar da Goje ya shigar a gabanta na kalubalantar dakatar da shi da kuma korarsa daga APC.

Ko a ciki watan Mayu, kwamitin zartarwa na APC na kasa ya janye maganar korar Goje daga APC.

A cikin sanarwar da sakataren yada labarai na APC na kasa, Felix Morka ya fitar ya sanar da cewa, korar ta Goje an jingine ta a gefe har sai an yi nazari akan matakin da APC reshen jihar ya dauka.

Alkali Egwuatu ya tabbatar da cewa, korafin Goje na rashin yi masa adalci don ya kare kansa daga zarge-zargen da kwamitin ya yi masa, bai da wata hujja, domin kwamitin ya ba shi isashen lokaci don ya kare kansa.

Kotun ta ce Goje na sane da zarge-zargen da ake yi masa, musamman ganin cewa wata jarida ta wallafa zarge-zargen da ake yi masa, inda hakan ya ke da damar ya kare kansa da kuma ba shi damar lokaci da wurin da zai kare kansa.

A martanin da babban kwamitin APC na jihar Gombe ya yaba da hukuncin da kotun ta yanke.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI
Labarai

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Labarai

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
Next Post
Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.