• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Tabbatar Da Korar Goje Daga Jami’yyar APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da karar da Sanata Mohammed Danjuma Goje, ya shigar a gabanta na kalubalantar korara da kwamitin jami’yyar APC na mazabar Kashere da ke jihar Gombe ya yi masa.

Kwamitin ya dakatar da Goje ne daga baya kuma ya kore shi daga APC a watan Afrilu, 2023.

  • INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe
  • Masarautar Zazzau Ta Dakatar Da Marafan Yamman Zazzau Kan Daukar Doka A Hannunsa

Kwamitin ya kore shi ne, bisa zargin kin shiga ayyukan gangamin yakin neman zaben APC a dukkan matakai har da na yakin neman zaben shugaban kasa da kuma yi wa ‘yan takarar majalisar dikokin jihar da tarayya zagon kasa a lokacin yankin neman zaben.

Goje ya kuma ki yi wa shugabannin jami’yyar da’a da kuma kin yin biyayya ga mahukuntan da ke jagorantar jam’iyyar a jihar.

An kori Goje daga APC ne, bayan da kwamitin APC na mazabar Kashere ya mika rahotonsa na binciken zargin da ake yi wa Goje.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

A cikin rahoton kwamitin, ya gano cewa, zargin da ake yi wa Goje, ya tabbata, inda kwamitin ya bayar da shawarar a gaggauta dakatar da shi da kuma korarsa daga jam’iyyar.

Shugabancin APC na mazabar Kashere sun amince da rahoton kwamitin binciken, inda kuma babban kwamitin APC na jihar Gombe da sauran kwamitocin kananan hukumomi 11 na jihar, su ma suka amince da rahoton kwamitin da ya dakatar tare da korar Goje daga APC.

Bisa wannan dakatarwar ne da kuma korarsa, hakan ya sa Goje ya garzaya zuwa kotun don kalubalabatar matakin.

Sai dai, a hukuncin da alkalin babbar kotun da ke Abuja wadda mai shari’a alkali Obiora Egwatu ke jagoranta a zaman da ta yi a ranar Talata, ta yi fatali da karar da Goje ya shigar a gabanta na kalubalantar dakatar da shi da kuma korarsa daga APC.

Ko a ciki watan Mayu, kwamitin zartarwa na APC na kasa ya janye maganar korar Goje daga APC.

A cikin sanarwar da sakataren yada labarai na APC na kasa, Felix Morka ya fitar ya sanar da cewa, korar ta Goje an jingine ta a gefe har sai an yi nazari akan matakin da APC reshen jihar ya dauka.

Alkali Egwuatu ya tabbatar da cewa, korafin Goje na rashin yi masa adalci don ya kare kansa daga zarge-zargen da kwamitin ya yi masa, bai da wata hujja, domin kwamitin ya ba shi isashen lokaci don ya kare kansa.

Kotun ta ce Goje na sane da zarge-zargen da ake yi masa, musamman ganin cewa wata jarida ta wallafa zarge-zargen da ake yi masa, inda hakan ya ke da damar ya kare kansa da kuma ba shi damar lokaci da wurin da zai kare kansa.

A martanin da babban kwamitin APC na jihar Gombe ya yaba da hukuncin da kotun ta yanke.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGojeGombeHukunciKoraKotuMataki
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Za Ta Gurfanar Da Wadanda Ake Zargi Da Aikata Laifukan Zabe

Next Post

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

15 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

Jihohi 14 Da Za Su Fuskanci Ambaliyar Ruwa —NEMA

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.