• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Amsar Korafin Zabe Ta Amshi Koke-Koke 8 A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kotun Amsar Korafin Zabe Ta Amshi Koke-Koke 8 A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun amsar koke-koken zabe, ta amshi Koke-Koke guda takwas da suke kalubalantar zabukan kujerun ‘yan majalisun tarayya da na jihohi da hukumar zabe INEC ta gudanar a ranakun 25/2/2023 da 18/3/2023, a jihar Adamawa.

 

Rahotanni sunyi nuni da cewa ‘yan takarar jam’iyyar APC shida, suka garzaya kotun suna neman da kotun da rusa zabukan ‘yan majalisun tarayyar, da’aka bayyana da cewa na PDP ne.

  • Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Haka kuma cikin bukatun da ‘yan takarar jam’iyyar APC suka shigar gaban kotun sun bukaci da kotun da rusa zaben kujerar dan majalisar dattawa, mai wakiltar Adamawa ta tsakiya, da kakakin majalisar dokokin jihar Aminu Iya Abbas, yayi nasarar lashewa.

 

Labarai Masu Nasaba

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Kujerun ‘yan majalisun wakilan tarayyar da ‘yan takarar APC suka shigar gaban kotun sun hada da dan majalisa mai wakiltar kananan hukumomin Mubi ta kudu,Mubi ta arewa da Maiha da Jingi Rufai ya lashe da kuma kananan hukumomin Gombi,Hong da James Barka, ya lashe.

 

Sauran koke-koken da ke gaban kotun su ne; Abba Girei, (Muhammad Salihu) mai wakiltar Yola ya arewa, Yola ta kudu da Girei, da Muhammad Inuwa Bassi mai wakiltar kananan hukumomin Mayo-Belwa,Jada,Ganye da Toungo, da Zakaria Dauda Nyampa kananan hukumomin Michika da Madagali.

 

Da yake mika koken gaban kotun Sanata Abdul’aziz Nyako, ya roki kotun da ta rusa zaben kakakin majalisar dokokin jihar Aminu Iya Abbas da sauran mutum biyar da su ka yi nasara karkashin jam’iyyar PDP a zaben.

 

A bangare guda kuwa Rev. Amos Kumai Yohanna na jam’iyyar PDP ya na kalubalantar nasarar Sanata Ishaku Abbo, sanata mai wakiltar Adamawa ta arewa a karkashin jam’iyyar APC.

 

A takardar koken da Rev Amos ya gabatar gaban kotu mai lamba EPT/AD/SEN/02/2023, yayi zargin zaben Ishaka Cliff Abbo ya saba doka bisa dogaro da sabbin dokokin zaben 2022.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumi Na 8 A Wasu Birane

Next Post

Ba Da Yawunmu Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murna Ba – APC Kano 

Related

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum
Labarai

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

47 minutes ago
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
Labarai

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

1 hour ago
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
Labarai

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

2 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

12 hours ago
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 
Labarai

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

13 hours ago
Neja
Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

14 hours ago
Next Post
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

Ba Da Yawunmu Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murna Ba - APC Kano 

LABARAI MASU NASABA

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.