ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Neman Tsige Sarkin Zazzau

by Shehu Yahaya
10 months ago
Kotun

Kotun daukaka kara da ke zamanta a Jihar Kaduna, ta ayyana ranar Talata 22 ga watan Janairun 2025, domin yanke hukuncin karar da tsohon Wazirin Zazzau, Ibrahim Muhammad Aminu ya shigar gabanta, kan neman kotun ta tsige Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli daga karagar masarautar.

Aminu ya shigar da kara gaban kotun ne yana kalubalantar nadin Sarkin Zazzau, inda ya ce nadin an yi shi ne ba bisa ka’idojin zaben Sarkin Zazzau na 19.

  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano
  • Janar Murtala Mohammed: Ba Rabo Da Gwani Ba…

Tsohon Wazirin Zazzau wanda a wancan lokacin, yana daga cikin masu zaben Sarkin Zazzau, ya shigar da kara gaban kotun yana tuhumar mutane 13 da laifi wajen rashin bin dokan nada Sarki Ambasada Nuhu Bamalli.

ADVERTISEMENT

Daga cikin wadanda ya shigar da karar tasu, akwai Ahmad Nuhu Bamalli da Marigayi Limamin Kona, Malam Sani Aliyu da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad el-rufa da sauransu.

A yayin zaman kotun a shekarar 2023, lauya mai kare wadanda ake tuhuma, Barista Abdul Ibrahim, ya bayyana wa kotun cewa wanda ya kai karar bai da ikon jayayya da nadin sarki ko kuma neman tsige shi kan cewar ba shi a cikin wadanda suke da gadon sarautar, sannan kuma ba shi daga cikin wadanda suka tsaya takarar neman sarautar.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

Tsohon Wazirin Zazzau ya shigar da karar ne ta hannun lauyansa, Barisata B M Bello, inda yake kalubalantar cancantar nadin Ahmad Nuhu Bamalli kan kujerar sarautar Zazzau.

Hakan, ya sanya kotun ta bayyana cewa ranar 22 ga watan Janairun za ta kawo karshen rikicin.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
Labarai

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
Labarai

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Next Post
Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi

Yadda Jami'an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.