• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
Kungiyar masana'antu

Kungiyar Masana’antu ta Nijeriya (MAN) ta yi fatali da sake gabatar da harajin kaso hudu na (FOB) da hukumar Kwastam ta gabatar wanda ya fara aiki tun daga ranar 4 ga watan Agustan.

 

Darakta janar na MAN, Mista Segun Ajayi-Kadri, ya shaida hakan a Jihar Legas, wanda ya matakin ya saba wa dakatar da cajin da gwamnati ta yi tun da farko.

  • Mutane Da Dama Sun Tsere Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Neja Da Kwara
  • Bincike Ya Nuna Tarin Fuka Na Kashe Mutum 71,000 A Nijeriya Duk Shekara

Ya ce masana’antu suna kallon matakin zai kara janyo tsadar farashin shigo da kayayyakin sarrafa abubuwa, albarkatun kasa, injuna, da sauran kayayyakin da ba a samu a cikin gida ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ajayi-Kadri ya ce kungiyar ta yi cikakken nazari kan sake gabatar da harajin na FOB wanda ta tabbatar zai kara dagula lamura ne kawai da sake jefa masana’antu cikin mawuyacin hali.

 

“Gaskiyar lamarin ita ce, farashin kashi hudu cikin 100 na kamfanonin ya yi yawa fiye da yadda aka samu karin kashi bakwai cikin dari da kuma karin kashi daya cikin dari na harajin tsarin shigo da kayayyaki,” in ji shi.

 

Ya kara da cewa, a sauran kasashen yammacin Afirka kamar Ghana, Cote d’Iboire, da Senegal, ana tsare-tsaren da aka yi niyya ko tattara kudade a tsakanin kashi 0.5 zuwa kashi daya cikin 100 na FOB, tare da karin haraji kawai kan kayan alatu ko kuma wadanda ba su da muhimmanci a shigo da su.

 

“Hukuncin da hukumar kwastam ta Nijeriya ta yi na bai daya na kakaba harajin kashi hudu cikin 100 na FOB zai kara tsadar kasuwanci, da karfafa hanyoyin da ba a saba gani ba, zai haifar da karkatar da kaya da kuma kara tsanani,” in ji shugaban.

 

Ajayi-Kadri ya nemi gwamnatin tarayya da hukumar Kwastam da su janye matakin kakaba harajin kaso hudu na FOB domin kyautata tattalin arziki ko kuma a jinkita aiwatar da hakan har sai nan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Next Post
An Gabatar Da Shirin Musayar Al’adu Na “Echoes Of Peace” A Mexico

An Gabatar Da Shirin Musayar Al’adu Na “Echoes Of Peace” A Mexico

LABARAI MASU NASABA

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.