Cikin shekaru 30 da suka gabata, kwararru kusan 12,000 cikin kashi 10 ne suka ziyarci yankin Xizang mai cin gashin kansa na kudu maso yammacin kasar Sin, tun bayan fara aiwatar da shirin samarwa yankin taimako daga sauran yankuna.
A shekarar 1994, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta yanke wata muhimmiyar shawara ta samarwa Xizang taimako daga dukkan sassan kasar.
Karkashin shirin, an sanya wasu sassan gwamnatin tsakiya da na matakan larduna da kamfanonin mallakin gwamnati, bayar da taimako ga wasu yankunan na musammam na Xizang, domin karawa aikin raya yankin mai tsaunika kuzari. (Fa’iza Mustapaha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp