• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
Kwastam Ta Kama Kayan Fasa Kwauri Da Kudinsu Ya Kai Miliyan 78.6 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa (NCS) a Jihar Kebbi, ta kama wasu kayayyakin fasa kwauri da kudinsu ya kai Naira miliyan 78.6 a watan Oktoban 2022 a jihar.

Shugaban hukumar Kwastam, Mista Joseph Attah ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai a kan ayyukan hukumar na watan Oktoba a Birnin Kebbi.

  • Shugaba Xi Zai Gabatar Da Jawabi A Yayin Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 5
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Samar Da Fa’ida A Zahiri Ga Jama’ar Afirka

Ya ce rundunar ta samu nasarori a cikin muhimman ayyukan da suka shafi aikin dakile fasa kwauri, ta samar da kudaden shiga da kuma saukaka kasuwanci.

A cewarsa: “An ci gaba da samun karuwar kudaden shiga na hukumar. A tsawon lokacin da ake bitar, mun samar da zunzurutun kudi har Naira miliyan 162.2 a matsayin kudaden shiga daga harajin shigo da kayayyaki. Wannan shi ne mafi girma tun bayan bude iyakar ta Kamba da ke a Jihar ta Kebbi.

“Rundunar ta kuma taimaka wajen fitar da kayayyakin da ake sarrafa su a cikin gida na sama da Naira biliyan 2 a daidai lokacin da ake gudanar da bincike,” in ji Attah.

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Ya ce, rundunar ta umurci jami’ansu da su kara sanya ido a cikin lungu da sako na lungu da sako na ruwa a kokarinsu na dakile ayyukan fasa-kwauri a cikin lungu da sako na jihar.

“Saboda haka, kokarin da aka yi ya haifar da kama wasu kayayyaki iri-iri har 16 da suka hada da, fakiti 284 na kwamfutar tafi-da-gidanka, tabar wi-wi, motoci 4 da aka yi amfani da su, wadanda kuma akwai Motocin na shi ga jama’a kirar Honda guda biyu da aka yi amfani da su, da motar dizal guda daya da kuma babbar motar tifa.

“Sauran sun hada da, bale 139 na tufafin hannu, buhunan shinkafa 345 na kasar waje (kowanne kilogiram 50), lita 2,250 na man fetur (PMS), kwali 38 na man shafawa (bleaching cream), guda 80 na batura masu amfani da hasken rana, da dai sauransu.

“Abin da ake tsamani da za a biya na harajin kayayyakin da aka kama ya kai Naira miliyan 78.6,” inji shi.

Kazalika, Mista Attah ya bayyana kudurin rundunar na tabbatar da cewa wadanda suka zabi shigo da kaya ko fitar da su ta iyakar Kamba, sai bin ka’idojin da suka dace na dokar kasa.

“Za ku yarda da ni, cewa yayin da sauran kayayyakin da aka kama na da kididdigar kudi, ba za mu iya kididdige yawan barnar da kwayoyi masu hadari da sauran abubuwa ke haifarwa a cikin al’umma ba.”

Bugu da kari ya ce “Irin wannan abu idan aka fito da shi a cikin al’umma yana taimaka wa dukkan manyan laifukan da muke gani a cikin al’ummarmu.

“Za a mika tabar wi-wi ga hukumar NDLEA jihar Kebbi domin daukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Daga karshe dai, mista Joseph Attah ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da gudanar da aikin da aka ba su na dakile ayyukan fasa kwaurin ba tare da kasawa ba duk da kalubalen da ake fuskanta daga ‘yan kasa masu taimaka wa ga aikata miyagun laifuka a kan jami’ansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hukumar Hana Fasa KwauriKayayyakiKebbiMiliyoyin Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Zai Gabatar Da Jawabi A Yayin Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 5

Next Post

An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

6 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

7 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

9 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

10 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

11 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

13 hours ago
Next Post
An Kashe ‘Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

An Kashe 'Yan Bindiga A Kasuwa A Zamafara

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.