• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
3 years ago
Alkawari

Yanzu haka ana daf da cika shekaru 10 tun bayan taron farko na kwamitin kolin jamiyyar kwaminis ta kasar Sin na 18, tun bayan lokacin ne kuma sassan kasa da kasa ke zuba ido domin ganin yadda kasar Sin za ta dunkule tare da sauran sassan duniya, wajen cika alkawuran da ta dauka, na samarwa al’ummar duniya kyakkyawar makomar bai daya.

A iya cewa a bisa dukkanin shaidu “Kwalliya ta biya kudin sabulu”, domin kuwa kasar Sin ta shiga cikin hadakar kasashen duniya, wajen aiwatar da managartan shirye-shiryen samar da ci gaba, duk kuwa da kalubalen da duniya ta ci karo da su cikin wadannan shekaru.

  • Sin: Matakin Da Amurka Ta Dauka Babakere Ne Ta Fannin Kimiyya

Yayin ziyararsa ta farko a kasashen waje cikin watan Maris na shekarar 2013, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya zayyana burin kasarsa na bunkasa sabon salon cudanya, da hadin gwiwa da sauran sassan duniya, ta yadda za a kai ga cimma moriyar juna, wanda dukkanin bil adama zai ci moriyarsa.

Cikin shekarun baya bayan nan, kowa ya ga yadda kasar Sin ke kara azamar sauke nauyin dake wuyanta, na ingiza samar da ci gaba cikin lumana, da goyon bayan cudanyar sassa daban daban bisa adalci.

Sakamakon haka, mun ga yadda Sin ke ci gaba da ba da gudummawa a ayyukan wanzar da zaman lafiya da daidaito, da ba da gudummawar bunkasa raya tattalin arzikin duniya, da shiga ayyukan cimma moriyar bil adama na bai daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

Tuni manufar dake kunshe cikin shawarar nan ta “Ziri Daya da Hanya Daya” ko BRI, ta shiga lungu da sassan duniya, inda ta samar da zarafi karfafa kawance, da dinkewar Sin da sauran sassan duniya a fannin samar da ci gaba.

Kaza lika Sin ta shiga ayyukan yaki da annobar COVID-19, ta samar da gudummawar kayan kandagarki da na rigakafin annobar, matakin da ya samu babban yabo daga sassa daban daban.
Duba da wadannan shaidu na zahiri, muna iya cewa, Sin ta cika alkawuran da ta dauka ga duniya, musamman ma ga kawayen ta makusanta wato kasashe masu tasowa. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Shiga Tsakani Kan Rikicin Da Ya Kunno Kai Tsakanin Gwamnatin Kogi Da Dangote

Gwamnatin Kogi Ta Bai Wa Dangote Sa'o'i 48 Ya Kulle kamfanin Simintinsa Da Ke Obajana

LABARAI MASU NASABA

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.