• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
Afrika

An shiga makon tattauna batutuwan tattalin arziki da cinikayya da kuma hadin gwiwa da musayar al’adu tsakanin Sin da Afrika a lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, a jiya Litinin, inda aka yi kira da zurfafa hadin gwiwar bangarorin biyu.

Zan iya cewa kasashen Afrika sun yi dace, inda wannan taro ke gudana jim kadan bayan kammalar taron kolin JKS karo na 20, inda Sin ta saita wata sabuwar akiblar neman ci gaba da zamanantar da kanta.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa

Dacen da suka yi kuwa shi ne, akwai tarin sabbin darasin da ya kamata su dauka daga sabon tafarkin da Sin ta dauka na raya kanta, baya ga cin gajiyar kudurinta na kara fadada bude kofarta da habaka kasuwanci da kasashen waje.

Wannan taro, kamar sauran tarukan da Sin kan shirya, wata dama ce ga kasashen Afrika ta jan hankalin kamfanonin kasar Sin su zuba jari ko fadada ayyukansu a kasashensu.

Kasashen Afrika na da albarkatu da ba a sarrafawa, kasar Sin kuma, na da tarin fasahohi da gogewa a fannin kirkire-kirkire, wanda zai zama hadin gwiwar moriyar juna, da zai kai kasashen Afrika ga amfani da dimbin arzikin da suke da shi, inda za su iya samun ci gaba har ma da kyautata rayuwar jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Sanin cewa kasar Sin babbar kasuwa ce, ba sabon abu ba ne, don haka fadada kasuwanci da kasar, babbar riba ce.

A irin wannan taro ne ya kamata kasashen Afrika su gano abun da ake bukata a kasar Sin kuma su hada gwiwa da kamfanonin kasar domin su taimaka musu fitar da hajojinsu da cin gajiyar babbar kasuwar kasar.

Duniya ta riga ta san yadda Sin take goyon bayan nahiyar Afrika, take kuma kara jan kasashen nahiyar a jiki domin su koyi dabarun raya kansu. Yadda ake kara zurfafa hulda tsakanin bangarorin biyu, na bukatar karin hadin gwiwa da musayar al’adu domin fahimtar juna ta yadda za a toshe duk wata kafa ta baraka a tsakaninsu, ta hakan ne kuma zuri’o’in Sin da Afrika na gaba, za su kasance tamkar ’yan uwa.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Next Post
Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 37 Da Jikkata Wasu Da Dama A Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 37 Da Jikkata Wasu Da Dama A Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.