• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautata Musayar Al’Adu Zai Toshe Duk Wata Kafa Ta Baraka Tsakanin Sin Da Afrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An shiga makon tattauna batutuwan tattalin arziki da cinikayya da kuma hadin gwiwa da musayar al’adu tsakanin Sin da Afrika a lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, a jiya Litinin, inda aka yi kira da zurfafa hadin gwiwar bangarorin biyu.

Zan iya cewa kasashen Afrika sun yi dace, inda wannan taro ke gudana jim kadan bayan kammalar taron kolin JKS karo na 20, inda Sin ta saita wata sabuwar akiblar neman ci gaba da zamanantar da kanta.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa

Dacen da suka yi kuwa shi ne, akwai tarin sabbin darasin da ya kamata su dauka daga sabon tafarkin da Sin ta dauka na raya kanta, baya ga cin gajiyar kudurinta na kara fadada bude kofarta da habaka kasuwanci da kasashen waje.

Wannan taro, kamar sauran tarukan da Sin kan shirya, wata dama ce ga kasashen Afrika ta jan hankalin kamfanonin kasar Sin su zuba jari ko fadada ayyukansu a kasashensu.

Kasashen Afrika na da albarkatu da ba a sarrafawa, kasar Sin kuma, na da tarin fasahohi da gogewa a fannin kirkire-kirkire, wanda zai zama hadin gwiwar moriyar juna, da zai kai kasashen Afrika ga amfani da dimbin arzikin da suke da shi, inda za su iya samun ci gaba har ma da kyautata rayuwar jama’a.

Labarai Masu Nasaba

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sanin cewa kasar Sin babbar kasuwa ce, ba sabon abu ba ne, don haka fadada kasuwanci da kasar, babbar riba ce.

A irin wannan taro ne ya kamata kasashen Afrika su gano abun da ake bukata a kasar Sin kuma su hada gwiwa da kamfanonin kasar domin su taimaka musu fitar da hajojinsu da cin gajiyar babbar kasuwar kasar.

Duniya ta riga ta san yadda Sin take goyon bayan nahiyar Afrika, take kuma kara jan kasashen nahiyar a jiki domin su koyi dabarun raya kansu. Yadda ake kara zurfafa hulda tsakanin bangarorin biyu, na bukatar karin hadin gwiwa da musayar al’adu domin fahimtar juna ta yadda za a toshe duk wata kafa ta baraka a tsakaninsu, ta hakan ne kuma zuri’o’in Sin da Afrika na gaba, za su kasance tamkar ’yan uwa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Afirka Na Yin Tasiri Mai Yakini A Duniya

Next Post

Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 37 Da Jikkata Wasu Da Dama A Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

Related

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming
Daga Birnin Sin

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

3 hours ago
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

4 hours ago
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

5 hours ago
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba
Daga Birnin Sin

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

5 hours ago
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

6 hours ago
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
Daga Birnin Sin

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

6 hours ago
Next Post
Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 37 Da Jikkata Wasu Da Dama A Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

Hatsarin Mota Ya Halaka Mutum 37 Da Jikkata Wasu Da Dama A Hanyar Damaturu Zuwa Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

An Bude Baje Kolin Kayayyakin Sin Da Kudancin Asiya Karo Na 9 A Kunming

June 19, 2025
Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

Sin Za Ta Hanzarta Duba Bukatun Samun Lasisin Fitar Da Ma’adanan “Rare Earth” Zuwa Ketare

June 19, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 24 A Katsina

June 19, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kai Samame Fitattun Wuraren Shaye-shaye, Ta Cafke Mutane 19 A Kano

June 19, 2025
Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho

June 19, 2025
Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

Yunkurin Tauye Ci Gaban Fasahar Kera “Chips” Ta Sin Ba Zai Haifar Da Da Mai Ido Ba

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

Gwamnatin Tarayya Da Jamus Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Yuro Miliyan 20 A Ɓangaren Makamashi

June 19, 2025
Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki

June 19, 2025
Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.