• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyawun Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyawun Alkawari Cikawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da duniya ke ci gaba da fama da annobar COVID-19, a hannu guda kuma hukumomi da masana a fannin yaki da sauyin yanayi na yin gargadi game da yadda yunwa da fari da sauran bala’u daga indallahi za su iya addabar sassan duniya.

Kuma ana iya ganin haka a wasu sassa na duniya dake fama da matsaloli na ambaliyar ruwa ko mahaukaciyar guguwa dake tafe da ruwan sama da ma fari a wasu sassa na nahiyar Afirka da makamantansu.

  • Wang Yi Da Blinken Sun Tattauna Ta Wayar Tarho Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Masana dai sun sha yin gargadi tun ma kafin bullar annobar cutar COVID-19 ta zama wani batu na daban cewa, za a fuskanci mummunan matsalar jin kai da ba a taba gani irinta ba, tun a lokacin yakin duniya na biyu, saboda wasu dalilai.

Na baya-bayan shi ne, kiran da hukumomin agaji da dama suka yi na gaggauta samar da karin kudade da shugabanci na-gari, don tinkarar gagarumar matsalar ayyukan jin kai dake fuskantar miliyoyin mutanen dake zaune a shiyyar gabashin Afrika sanadiyyar matsanancin fari, har ma aka yi kashedin cewa, muddin aka yi jinkiri to, babu makawa rayukan jama’a da dama na iya salwanta.

Haka ma kwararru daga nahiyar Afirka sun bukaci kasashen da suka ci gaba, da su cika alkawuran da suka dauka, na samar da isassun kudaden gudanar da ayyukan dakile sauyin yanayi, yayin taron COP27 da zai gudana a birnin Sharm El-Sheikh na kasar Masar.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

A cewarsu kasashen da suka ci gaba ne ke fitar da kaso mafi yawa na iskar Carbon mai dumama yanayin duniyarmu, don haka ya dace su samar da kudaden rage tasirin sauyin yanayi ga kasashe masu tasowa, wadanda ke dandana kuda sakamakon rashin karfinsu na tunkarar wannan kalubale. Domin idan babu kira to me zai ci gawayi.

Ko da a watannin da suka gabata ma, kasashen Afika da dama sun sha fama da wasu daga cikin munanan tasirin sauyin yanayi, ciki har da ambaliyar ruwa a Najeriya, da fari a yankin kahon Afirka.

Saboda haka, nahiyar Afirka na fatan sauran sassan duniya za su fahimci mummunan tasirin da nahiyar ke fama da shi daga sauyin yanayi.

Idan ba a manta ba kasashe masu wadata sun yi alkawarin baiwa nahiyar Afirka gudummawar dalar Amurka biliyan 100 a duk shekara, domin gudanar da ayyukan dakile tasirin sauyin yanayi, amma har yanzu shiru ka ke ji, wai malam ya ci shirwa.

Idan har duniya na fatan magance matsalar tasirin sauyin yanayi, ya dace taron na wannan karo, ya duba alkawuran da aka yi yayin taron COP26 na birnin Glasgow, ta yadda za a fitar da kyakkyawan tsarin aiwatarwa, wanda kowa zai amince da shi. Domin kyan alkawari aka ce cikawa. Kuma wannan shi ne dattaku.

Matsalar sauyin yanayi, na kara sanya tarin jama’a kauracewa muhallansu lamarin dake sanadiyyar fadawar karin mutane cikin yanayin tsananin bukata.

Wannan ne ma, ya sa masu fashin baki ke cewa, yanzu ne lokacin da ya dace na daukar matakai, domin kaucewa fadawar miliyoyin al’ummomi, musamman dake shiyyar gabashin Afrika cikin garari. Aka ce da zafi-zafi kan bugi karfe. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Yi Fada Da Dan Takarar Mataimakin Gwamnan Kano Ba – Doguwa

Next Post

Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

1 day ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

LABARAI MASU NASABA

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.