• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya ya ce, matsalar da ta addabi hanyar Gombe zuwa Bauchi na yawan rugujewar gadoji da kuma yankewar hanyar sun sa hanyar ta zama tarkon mutuwa ga matafiya a Arewa Maso Gabas.

 

Don haka, ya yi kiira da babban murya ga Gwamnatin tarayya ta dauki matakin gaggawa don magance matsalar cikin kankanin lokaci.

  • Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3

Hanyar ce dai ta hade Jihohin Gombe da Bauchi da Taraba da wasu yankunan Jihar Borno, hakan yasa ta kasance muhimmiya ga harkokin sufurin kayayyaki da zirga-zirgar jama’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

A ziyarar gani da ido da ya kai wurin da gadar ta yanke a Kalajanga na karamar hukumar Kirfi ta Jihar Bauchi a jiya, Gwamna Inuwa ya jaddada muhimmancin hanyar ga harkokin tattalin arziki da zamantakewar al’ummar yankin Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kwatanta hanyar a matsayin wata muhimmiyar jijiyar dake hade muhimman yankunan kasar nan, ya na mai bayyana muhimmiyar rawar da take takawa a harkokin tattalin arzikin jama’ar yankin.

 

“Wannar hanya kamar jijiya ce dake hada zuciya da kwakwalwa, wacce ke samar da jini da iskar numfashi, idan ta yanke babu wani bangare na jiki da zai iya aiki, wannan ita ce hanyar da take zuwa wannan yanki daga sassan kasar nan.”

Hanyar Bauchi

Ya kara da cewa “Na yi imanin cewa gwamnan Bauchi ya na nan, kuma kar ku yi mamaki gobe ku ga gwamnan Adamawa ko Borno a nan saboda mahimmancin wannar hanyar ga dokacin wannan yankin.”

 

Ya kuma jaddada bukatar gyara da sake gina hanyar, inda ya ce hanyar ta kusan shekaru 50 da ginawa, don haka tana bukatar karin gadoji da garanbawul baki daya.

 

Gwamna Inuwa ya ce zagayawa ta wasu hanyoyi yana tattare da marin kashe kudi da bata lokaci, yana mai jaddada bukatar kammala aikin gyaran cikin gaggawa don saukaka zirga-zirgar ababen hawa a fadin jihohin na Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin hanyar ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa ba ga Jihar Gombe kadai ba, har ma da yankin arewa maso gabas baki daya, yana mai alakanta rashin kyan hanyar ga matsalolin muhalli da karuwar aikace-aikacen jama’a.

 

Ya ce tun bayan hawansa mulki yake ta bin diddigin yadda hanyar za ta samu gyaran da ya kamata.

 

“A baya na ziyarci ma’aikatar ayyuka kusan sau hudu kan wannan batu, ina kokarin jawo hankalin Gwamnatin tarayya kan ta dauki matakin gaggawa don magance wannar matsala kwata-kwata. Ko a jiya ma sai da na kira Babban Sakataren Ma’aikatar Ayyuka na Tarayya kan batun.

 

“Dole ne Gwamnatin Tarayya ta shigo cikin lamarin da gaggawa ta magance wannar matsala saboda rayuwar miliyoyin jama’a ta ta’allaka da wannar hanya”, yana mai bayyana lamarin a matsayin wadda ke buƙatar daukin gaggawa.

Hanyar Bauchi

Gwamna Inuwa ya kuma yi alkawarin kara kaimi ga shugaban kasa, don samar da mafita ta din-din-din ga matsalar.

 

Da yake yabawa da ayyukan da hukumar kula da hanyoyi ta tarayya (FERMA) ke ci gaba da yi na kokarin samar da mafita ta wucin gadi, ya bayyana fatan cewa hakan zai sa a samu mafita cikin ‘yan kwanaki.

 

Da yake jawabi a madadin ma’aikatar ayyuka ta tarayya, jami’in ma’aikatar dake kula da aikin, Engr. Bitrus Dauda, ya ce ma’aikatar na yin duk mai yiwuwa don gyaran hanyar, tare da bada tabbacin kara matsin lamba kan bukatar gina karin gadoji a kan hanyar.

 

Ya ce, “Tun ba yau ba muka mika koke ga ma’aikatar ayyuka ta tarayya kan yanayin hanyar musamman wuraren da ake bukatar manyan gadoji, yanzu muna jiran a ba mu tsarin aikin ne don aiwatar da shi”.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamandan hukumar Kiyaye Hatsurra ta Tarayyar Reshen Jihar Bauchi, Mista Patrick Ikaba, ya ce rundunar ta kammala shirye-shiryen sanya alamun gargadi da ankararwa a wurare masu mahimmanci don magance hatsura, tare da shawartar masu ababen hawa da sauran masu amfani da hanyar su koma bin wassu hanyoyin daban don kare lafiya da rayukansu.

 

Yankewar gadan na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Lahadi bayan da aka shafe sa’o’i ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, wanda ya yi sanadiyar ambaliyar ruwa da ta fi karfin gadar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Muhalli Ta Farko Ta Kasar Sin Za Ta Amfani Duniya Baki Daya

Next Post

Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

Related

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

3 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

4 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

15 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

16 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

17 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

20 hours ago
Next Post
Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.