• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Hanyar Bauchi

Gwamnan Jihar Gombe kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya ya ce, matsalar da ta addabi hanyar Gombe zuwa Bauchi na yawan rugujewar gadoji da kuma yankewar hanyar sun sa hanyar ta zama tarkon mutuwa ga matafiya a Arewa Maso Gabas.

 

Don haka, ya yi kiira da babban murya ga Gwamnatin tarayya ta dauki matakin gaggawa don magance matsalar cikin kankanin lokaci.

  • Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3

Hanyar ce dai ta hade Jihohin Gombe da Bauchi da Taraba da wasu yankunan Jihar Borno, hakan yasa ta kasance muhimmiya ga harkokin sufurin kayayyaki da zirga-zirgar jama’a.

 

LABARAI MASU NASABA

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

A ziyarar gani da ido da ya kai wurin da gadar ta yanke a Kalajanga na karamar hukumar Kirfi ta Jihar Bauchi a jiya, Gwamna Inuwa ya jaddada muhimmancin hanyar ga harkokin tattalin arziki da zamantakewar al’ummar yankin Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kwatanta hanyar a matsayin wata muhimmiyar jijiyar dake hade muhimman yankunan kasar nan, ya na mai bayyana muhimmiyar rawar da take takawa a harkokin tattalin arzikin jama’ar yankin.

 

“Wannar hanya kamar jijiya ce dake hada zuciya da kwakwalwa, wacce ke samar da jini da iskar numfashi, idan ta yanke babu wani bangare na jiki da zai iya aiki, wannan ita ce hanyar da take zuwa wannan yanki daga sassan kasar nan.”

Hanyar Bauchi

Ya kara da cewa “Na yi imanin cewa gwamnan Bauchi ya na nan, kuma kar ku yi mamaki gobe ku ga gwamnan Adamawa ko Borno a nan saboda mahimmancin wannar hanyar ga dokacin wannan yankin.”

 

Ya kuma jaddada bukatar gyara da sake gina hanyar, inda ya ce hanyar ta kusan shekaru 50 da ginawa, don haka tana bukatar karin gadoji da garanbawul baki daya.

 

Gwamna Inuwa ya ce zagayawa ta wasu hanyoyi yana tattare da marin kashe kudi da bata lokaci, yana mai jaddada bukatar kammala aikin gyaran cikin gaggawa don saukaka zirga-zirgar ababen hawa a fadin jihohin na Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin hanyar ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa ba ga Jihar Gombe kadai ba, har ma da yankin arewa maso gabas baki daya, yana mai alakanta rashin kyan hanyar ga matsalolin muhalli da karuwar aikace-aikacen jama’a.

 

Ya ce tun bayan hawansa mulki yake ta bin diddigin yadda hanyar za ta samu gyaran da ya kamata.

 

“A baya na ziyarci ma’aikatar ayyuka kusan sau hudu kan wannan batu, ina kokarin jawo hankalin Gwamnatin tarayya kan ta dauki matakin gaggawa don magance wannar matsala kwata-kwata. Ko a jiya ma sai da na kira Babban Sakataren Ma’aikatar Ayyuka na Tarayya kan batun.

 

“Dole ne Gwamnatin Tarayya ta shigo cikin lamarin da gaggawa ta magance wannar matsala saboda rayuwar miliyoyin jama’a ta ta’allaka da wannar hanya”, yana mai bayyana lamarin a matsayin wadda ke buƙatar daukin gaggawa.

Hanyar Bauchi

Gwamna Inuwa ya kuma yi alkawarin kara kaimi ga shugaban kasa, don samar da mafita ta din-din-din ga matsalar.

 

Da yake yabawa da ayyukan da hukumar kula da hanyoyi ta tarayya (FERMA) ke ci gaba da yi na kokarin samar da mafita ta wucin gadi, ya bayyana fatan cewa hakan zai sa a samu mafita cikin ‘yan kwanaki.

 

Da yake jawabi a madadin ma’aikatar ayyuka ta tarayya, jami’in ma’aikatar dake kula da aikin, Engr. Bitrus Dauda, ya ce ma’aikatar na yin duk mai yiwuwa don gyaran hanyar, tare da bada tabbacin kara matsin lamba kan bukatar gina karin gadoji a kan hanyar.

 

Ya ce, “Tun ba yau ba muka mika koke ga ma’aikatar ayyuka ta tarayya kan yanayin hanyar musamman wuraren da ake bukatar manyan gadoji, yanzu muna jiran a ba mu tsarin aikin ne don aiwatar da shi”.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamandan hukumar Kiyaye Hatsurra ta Tarayyar Reshen Jihar Bauchi, Mista Patrick Ikaba, ya ce rundunar ta kammala shirye-shiryen sanya alamun gargadi da ankararwa a wurare masu mahimmanci don magance hatsura, tare da shawartar masu ababen hawa da sauran masu amfani da hanyar su koma bin wassu hanyoyin daban don kare lafiya da rayukansu.

 

Yankewar gadan na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Lahadi bayan da aka shafe sa’o’i ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, wanda ya yi sanadiyar ambaliyar ruwa da ta fi karfin gadar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

IMF
Labarai

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
katsina
Labarai

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Next Post
Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

LABARAI MASU NASABA

IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.