• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe kuma shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya ya ce, matsalar da ta addabi hanyar Gombe zuwa Bauchi na yawan rugujewar gadoji da kuma yankewar hanyar sun sa hanyar ta zama tarkon mutuwa ga matafiya a Arewa Maso Gabas.

 

Don haka, ya yi kiira da babban murya ga Gwamnatin tarayya ta dauki matakin gaggawa don magance matsalar cikin kankanin lokaci.

  • Za A Gyara Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Da Ta Yanke Cikin Kwana 3

Hanyar ce dai ta hade Jihohin Gombe da Bauchi da Taraba da wasu yankunan Jihar Borno, hakan yasa ta kasance muhimmiya ga harkokin sufurin kayayyaki da zirga-zirgar jama’a.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

A ziyarar gani da ido da ya kai wurin da gadar ta yanke a Kalajanga na karamar hukumar Kirfi ta Jihar Bauchi a jiya, Gwamna Inuwa ya jaddada muhimmancin hanyar ga harkokin tattalin arziki da zamantakewar al’ummar yankin Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kwatanta hanyar a matsayin wata muhimmiyar jijiyar dake hade muhimman yankunan kasar nan, ya na mai bayyana muhimmiyar rawar da take takawa a harkokin tattalin arzikin jama’ar yankin.

 

“Wannar hanya kamar jijiya ce dake hada zuciya da kwakwalwa, wacce ke samar da jini da iskar numfashi, idan ta yanke babu wani bangare na jiki da zai iya aiki, wannan ita ce hanyar da take zuwa wannan yanki daga sassan kasar nan.”

Hanyar Bauchi

Ya kara da cewa “Na yi imanin cewa gwamnan Bauchi ya na nan, kuma kar ku yi mamaki gobe ku ga gwamnan Adamawa ko Borno a nan saboda mahimmancin wannar hanyar ga dokacin wannan yankin.”

 

Ya kuma jaddada bukatar gyara da sake gina hanyar, inda ya ce hanyar ta kusan shekaru 50 da ginawa, don haka tana bukatar karin gadoji da garanbawul baki daya.

 

Gwamna Inuwa ya ce zagayawa ta wasu hanyoyi yana tattare da marin kashe kudi da bata lokaci, yana mai jaddada bukatar kammala aikin gyaran cikin gaggawa don saukaka zirga-zirgar ababen hawa a fadin jihohin na Arewa Maso Gabas.

 

Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin hanyar ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa ba ga Jihar Gombe kadai ba, har ma da yankin arewa maso gabas baki daya, yana mai alakanta rashin kyan hanyar ga matsalolin muhalli da karuwar aikace-aikacen jama’a.

 

Ya ce tun bayan hawansa mulki yake ta bin diddigin yadda hanyar za ta samu gyaran da ya kamata.

 

“A baya na ziyarci ma’aikatar ayyuka kusan sau hudu kan wannan batu, ina kokarin jawo hankalin Gwamnatin tarayya kan ta dauki matakin gaggawa don magance wannar matsala kwata-kwata. Ko a jiya ma sai da na kira Babban Sakataren Ma’aikatar Ayyuka na Tarayya kan batun.

 

“Dole ne Gwamnatin Tarayya ta shigo cikin lamarin da gaggawa ta magance wannar matsala saboda rayuwar miliyoyin jama’a ta ta’allaka da wannar hanya”, yana mai bayyana lamarin a matsayin wadda ke buƙatar daukin gaggawa.

Hanyar Bauchi

Gwamna Inuwa ya kuma yi alkawarin kara kaimi ga shugaban kasa, don samar da mafita ta din-din-din ga matsalar.

 

Da yake yabawa da ayyukan da hukumar kula da hanyoyi ta tarayya (FERMA) ke ci gaba da yi na kokarin samar da mafita ta wucin gadi, ya bayyana fatan cewa hakan zai sa a samu mafita cikin ‘yan kwanaki.

 

Da yake jawabi a madadin ma’aikatar ayyuka ta tarayya, jami’in ma’aikatar dake kula da aikin, Engr. Bitrus Dauda, ya ce ma’aikatar na yin duk mai yiwuwa don gyaran hanyar, tare da bada tabbacin kara matsin lamba kan bukatar gina karin gadoji a kan hanyar.

 

Ya ce, “Tun ba yau ba muka mika koke ga ma’aikatar ayyuka ta tarayya kan yanayin hanyar musamman wuraren da ake bukatar manyan gadoji, yanzu muna jiran a ba mu tsarin aikin ne don aiwatar da shi”.

 

Shi ma a nasa jawabin, kwamandan hukumar Kiyaye Hatsurra ta Tarayyar Reshen Jihar Bauchi, Mista Patrick Ikaba, ya ce rundunar ta kammala shirye-shiryen sanya alamun gargadi da ankararwa a wurare masu mahimmanci don magance hatsura, tare da shawartar masu ababen hawa da sauran masu amfani da hanyar su koma bin wassu hanyoyin daban don kare lafiya da rayukansu.

 

Yankewar gadan na baya-bayan nan ya faru ne a ranar Lahadi bayan da aka shafe sa’o’i ana ruwan sama kamar da bakin kwarya, wanda ya yi sanadiyar ambaliyar ruwa da ta fi karfin gadar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Muhalli Ta Farko Ta Kasar Sin Za Ta Amfani Duniya Baki Daya

Next Post

Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Hanyar Bauchi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

Jakadan Argentina: “Ya San Mene Ne Abubuwan Da Jama’a Ke Bukata”

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.