• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Kar A Fake Da Batun Dimokuradiyya Don Neman Biyan Bukatar Kai

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A yau Litinin, ma’aikatar harkokin wajen Sin ta gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda a gun taron wani dan jarida ya yi tambayar da ta shafi taron kolin dimokuradiyya da Koriya ta Kudu ke karbar bakunci yanzu haka.

Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya bayyana cewa, a ko da yaushe bangaren Sin yana adawa da matakin raba kasashe zuwa rukunai daban daban bisa tunaninsu na siyasa, da fakewa da maganar dimokuradiyya a kokarin neman biyan bukatar kai.

  • Sin Ta Shirya Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2
  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang

Lin ya kara da cewa, a halin yanzu, abun da sassan kasa da kasa ke bukata ba wai haifar da rarrabuwar kai da sunan dimokuradiyya ba ne, maimakon haka ana fatan karfafa hadin gwiwa, da inganta dangantakar dimokuradiyya tsakanin sassan kasa da kasa bisa ka’idojin MDD.

Game da yadda wasu mutane daga bangaren yankin Taiwan na kasar Sin suka halarci taron kolin na dimokuradiyya kuwa, Lin Jian ya bayyana cewa, bangaren Sin na matukar adawa da yadda Koriya ta Kudu ta gayyaci hukumomin yankin Taiwan zuwa taron.

Ya ce kasar Sin daya tak ce a duniya, kana yankin Taiwan bangare ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba. Kaza lika duk wani bangare na ketare, dake tsoma hannu cikin harkokin gidan Sin, ta hanyar nuna goyon baya ga manufar wai “’yancin kan Taiwan”, zai sha kaye.

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Game da zartas da daftarin kudurin matakan kawar da tsoron Musulunci a babban taron MDD, Lin ya ce, Sin tana cikin kasashen da suka dauki nauyin tsara daftarin kudurin, inda ta yi maraba da zartas da daftarin kudurin. Ya ce bangaren Sin na ganin cewa, tayar da rikicin al’adu, da kuma kai hare-hare ga mabiya addinai, ba abun da za su haifar wa duniya illa rabuwar kawuna da kuma tashin hankali.

Game da matsayar Sin kan rikicin Rasha da Ukraine kuwa, Lin ya bayyana cewa, bangaren Sin na goyon bayan gudanar da taron tattaunawa na kasa da kasa, wanda bangarorin Rasha da Ukraine suka amince da shi. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Next Post
Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Kaduna Za Ta Kashe Naira Biliyan 11.4 Wajen Bayar Da Tallafi

Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Kaduna Za Ta Kashe Naira Biliyan 11.4 Wajen Bayar Da Tallafi

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

EFCC Ta Ƙwato Kadarorin Naira Biliyan 500 A Ƙarƙashin Gwamnatin Tinubu – Shettima

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.