• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Kar A Fake Da Batun Dimokuradiyya Don Neman Biyan Bukatar Kai

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Kar A Fake Da Batun Dimokuradiyya Don Neman Biyan Bukatar Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Litinin, ma’aikatar harkokin wajen Sin ta gudanar da taron manema labarai na yau da kullum, inda a gun taron wani dan jarida ya yi tambayar da ta shafi taron kolin dimokuradiyya da Koriya ta Kudu ke karbar bakunci yanzu haka.

Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya bayyana cewa, a ko da yaushe bangaren Sin yana adawa da matakin raba kasashe zuwa rukunai daban daban bisa tunaninsu na siyasa, da fakewa da maganar dimokuradiyya a kokarin neman biyan bukatar kai.

  • Sin Ta Shirya Harba Tauraron Dan Adam Na Queqiao-2
  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang

Lin ya kara da cewa, a halin yanzu, abun da sassan kasa da kasa ke bukata ba wai haifar da rarrabuwar kai da sunan dimokuradiyya ba ne, maimakon haka ana fatan karfafa hadin gwiwa, da inganta dangantakar dimokuradiyya tsakanin sassan kasa da kasa bisa ka’idojin MDD.

Game da yadda wasu mutane daga bangaren yankin Taiwan na kasar Sin suka halarci taron kolin na dimokuradiyya kuwa, Lin Jian ya bayyana cewa, bangaren Sin na matukar adawa da yadda Koriya ta Kudu ta gayyaci hukumomin yankin Taiwan zuwa taron.

Ya ce kasar Sin daya tak ce a duniya, kana yankin Taiwan bangare ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba. Kaza lika duk wani bangare na ketare, dake tsoma hannu cikin harkokin gidan Sin, ta hanyar nuna goyon baya ga manufar wai “’yancin kan Taiwan”, zai sha kaye.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Game da zartas da daftarin kudurin matakan kawar da tsoron Musulunci a babban taron MDD, Lin ya ce, Sin tana cikin kasashen da suka dauki nauyin tsara daftarin kudurin, inda ta yi maraba da zartas da daftarin kudurin. Ya ce bangaren Sin na ganin cewa, tayar da rikicin al’adu, da kuma kai hare-hare ga mabiya addinai, ba abun da za su haifar wa duniya illa rabuwar kawuna da kuma tashin hankali.

Game da matsayar Sin kan rikicin Rasha da Ukraine kuwa, Lin ya bayyana cewa, bangaren Sin na goyon bayan gudanar da taron tattaunawa na kasa da kasa, wanda bangarorin Rasha da Ukraine suka amince da shi. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Aikin Karkata Akalar Ruwa Daga Kudu Zuwa Arewacin Sin Ya Amfani Sama Da Mutane Miliyan 176

Next Post

Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Kaduna Za Ta Kashe Naira Biliyan 11.4 Wajen Bayar Da Tallafi

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

9 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

10 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

11 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

12 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

13 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

15 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Kaduna Za Ta Kashe Naira Biliyan 11.4 Wajen Bayar Da Tallafi

Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Kaduna Za Ta Kashe Naira Biliyan 11.4 Wajen Bayar Da Tallafi

LABARAI MASU NASABA

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.