• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta umurci kwamitinta mai kula da harkokin man fetur da ya binciki kiran da aka yi na korar Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa abin da ta kira da kalaman cin fuska ga matatun man fetur na Nijeriya.

 

Wannan dai ya biyo bayan amincewa da kudiri kan “Bukatar gaggawar magance kalaman rashin da’a da shugaban hukumar NMDPRA ya furta, wanda dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Oredo na jihar Edo, Hon. Esosa Iyawe, a zauren majalisa a ranar Talata ya jagoranta.

  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro, Talauci A Arewa
  • Majalisa Ta Amince N70,000 A Matsayin Sabon Mafi Karancin Albashi

A kudirin, Iyawe ya bayyana cewa, ingancin man fetur na iya tasiri kan aikin injin, don haka, dole ana bukatar dizal ko man fetur mai ƙarancin sulphur ga kowane nau’ikan inji a kamfanoni, masana’antar wutar lantarki, tankunan ajiya, jiragen ruwa da duk wani inji mai babban aiki. Bugu da kari, yawaitar sulfur acikin man fetur yana haifar da lalacewa ga injuna kuma yana taimakawa wajen gurbata iska.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Ya kuma yi nuni da cewa, la’akari da irin hadurran da ke tattare da sinadarin Sulphur, gwamnatocin duniya sun dauki matakin daidaita shi ta hanyar gindaya ka’idojin da ake bukatar rage yawan hayakin wannan sinadari, wanda ake sa ran masu samar da dizal za su bi.

 

Ya sanar da cewa, a kwanakin baya, Shugaban Hukumar NMDPRA, ya bayyana cewa, man dizal da matatar Dangote ke samarwa bai kai wanda ake shigowa da shi kasar nan ba, kuma man da Matatar Dangote ke da shi na da sinadarin sulfur mai yawa.

 

Da take kare kanta, matatar Dangote ta bukaci a yi gwajin kayayyakinsu, wanda ‘yan majalisar suka je matatar da kansu don tabbatar da ingancin kayayyakin da matatar ke tacewa. Sakamakon binciken ya musanta zargin da shugaban NMDPRA ya yi.

 

Don haka, Iyawe ya nuna damuwarsa kan zargin da ake wa hukumar NMDPRA na ba da lasisi ga wasu ‘yan kasuwa da ke shigo da dizal mai yawan gaske a Nijeriya kuma gurbatacce, wanda kuma amfani da irin wadannan kayayyakin na haifar da babbar illa ga lafiya da asarar kudi ga ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Jaddadawa Manyan Jami’an USCBC Aniyar Sin Ta Zurfafa Gyare-gyare Da Kara Bude Kofa Ga Kasashen Waje

Next Post

Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

Related

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

25 minutes ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

2 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

5 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

8 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

1 day ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

2 days ago
Next Post
Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.