• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote

by Sulaiman
1 year ago
NMDPRA

Majalisar Wakilai ta umurci kwamitinta mai kula da harkokin man fetur da ya binciki kiran da aka yi na korar Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa abin da ta kira da kalaman cin fuska ga matatun man fetur na Nijeriya.

 

Wannan dai ya biyo bayan amincewa da kudiri kan “Bukatar gaggawar magance kalaman rashin da’a da shugaban hukumar NMDPRA ya furta, wanda dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Oredo na jihar Edo, Hon. Esosa Iyawe, a zauren majalisa a ranar Talata ya jagoranta.

  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro, Talauci A Arewa
  • Majalisa Ta Amince N70,000 A Matsayin Sabon Mafi Karancin Albashi

A kudirin, Iyawe ya bayyana cewa, ingancin man fetur na iya tasiri kan aikin injin, don haka, dole ana bukatar dizal ko man fetur mai ƙarancin sulphur ga kowane nau’ikan inji a kamfanoni, masana’antar wutar lantarki, tankunan ajiya, jiragen ruwa da duk wani inji mai babban aiki. Bugu da kari, yawaitar sulfur acikin man fetur yana haifar da lalacewa ga injuna kuma yana taimakawa wajen gurbata iska.

 

LABARAI MASU NASABA

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Ya kuma yi nuni da cewa, la’akari da irin hadurran da ke tattare da sinadarin Sulphur, gwamnatocin duniya sun dauki matakin daidaita shi ta hanyar gindaya ka’idojin da ake bukatar rage yawan hayakin wannan sinadari, wanda ake sa ran masu samar da dizal za su bi.

 

Ya sanar da cewa, a kwanakin baya, Shugaban Hukumar NMDPRA, ya bayyana cewa, man dizal da matatar Dangote ke samarwa bai kai wanda ake shigowa da shi kasar nan ba, kuma man da Matatar Dangote ke da shi na da sinadarin sulfur mai yawa.

 

Da take kare kanta, matatar Dangote ta bukaci a yi gwajin kayayyakinsu, wanda ‘yan majalisar suka je matatar da kansu don tabbatar da ingancin kayayyakin da matatar ke tacewa. Sakamakon binciken ya musanta zargin da shugaban NMDPRA ya yi.

 

Don haka, Iyawe ya nuna damuwarsa kan zargin da ake wa hukumar NMDPRA na ba da lasisi ga wasu ‘yan kasuwa da ke shigo da dizal mai yawan gaske a Nijeriya kuma gurbatacce, wanda kuma amfani da irin wadannan kayayyakin na haifar da babbar illa ga lafiya da asarar kudi ga ‘yan Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Next Post
Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.