• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta umurci kwamitinta mai kula da harkokin man fetur da ya binciki kiran da aka yi na korar Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NMDPRA), Farouk Ahmed, bisa abin da ta kira da kalaman cin fuska ga matatun man fetur na Nijeriya.

 

Wannan dai ya biyo bayan amincewa da kudiri kan “Bukatar gaggawar magance kalaman rashin da’a da shugaban hukumar NMDPRA ya furta, wanda dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Oredo na jihar Edo, Hon. Esosa Iyawe, a zauren majalisa a ranar Talata ya jagoranta.

  • ACF Ta Koka Da Rashin Tsaro, Talauci A Arewa
  • Majalisa Ta Amince N70,000 A Matsayin Sabon Mafi Karancin Albashi

A kudirin, Iyawe ya bayyana cewa, ingancin man fetur na iya tasiri kan aikin injin, don haka, dole ana bukatar dizal ko man fetur mai ƙarancin sulphur ga kowane nau’ikan inji a kamfanoni, masana’antar wutar lantarki, tankunan ajiya, jiragen ruwa da duk wani inji mai babban aiki. Bugu da kari, yawaitar sulfur acikin man fetur yana haifar da lalacewa ga injuna kuma yana taimakawa wajen gurbata iska.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Ya kuma yi nuni da cewa, la’akari da irin hadurran da ke tattare da sinadarin Sulphur, gwamnatocin duniya sun dauki matakin daidaita shi ta hanyar gindaya ka’idojin da ake bukatar rage yawan hayakin wannan sinadari, wanda ake sa ran masu samar da dizal za su bi.

 

Ya sanar da cewa, a kwanakin baya, Shugaban Hukumar NMDPRA, ya bayyana cewa, man dizal da matatar Dangote ke samarwa bai kai wanda ake shigowa da shi kasar nan ba, kuma man da Matatar Dangote ke da shi na da sinadarin sulfur mai yawa.

 

Da take kare kanta, matatar Dangote ta bukaci a yi gwajin kayayyakinsu, wanda ‘yan majalisar suka je matatar da kansu don tabbatar da ingancin kayayyakin da matatar ke tacewa. Sakamakon binciken ya musanta zargin da shugaban NMDPRA ya yi.

 

Don haka, Iyawe ya nuna damuwarsa kan zargin da ake wa hukumar NMDPRA na ba da lasisi ga wasu ‘yan kasuwa da ke shigo da dizal mai yawan gaske a Nijeriya kuma gurbatacce, wanda kuma amfani da irin wadannan kayayyakin na haifar da babbar illa ga lafiya da asarar kudi ga ‘yan Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi Ya Jaddadawa Manyan Jami’an USCBC Aniyar Sin Ta Zurfafa Gyare-gyare Da Kara Bude Kofa Ga Kasashen Waje

Next Post

Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

Related

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

18 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

23 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

1 day ago
Next Post
Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

Sin Ta Kara Adadin Sabbin Guraben Ayyukan Yi Miliyan 6.98 A Rabin Farko Na Shekarar Bana 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.