Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan kisan gilla da aka yi wa wasu mutane 13 da ba su ji ba ba su gani ba a Unguwan Rimi Basawa da ke karamar hukumar Sabon Gari ta Jihar Kaduna a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Majalisar ta umurci kwamitinta na wucin gadi da ke aiki kan kalubalen tsaro a jihar Filato da ya gudanar da bincike na musamman kan yadda ake ci gaba da kashe matafiya a hanya daya tare da bayar da rahoto cikin kwanaki 14.
- Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
- Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta
Wannan kudiri ya biyo bayan amincewa da kudirin da dan majalisa mai wakiltar mazabar Sabon Gari ta jihar Kaduna ya gabatar a karkashin al’amuran da ke bukatar kulawar gaggawa na majalisar, Sadiq Abdullahi, a zauren majalisar ranar Talata.
Da yake gabatar da kudirin, dan majalisar, Abdullahi ya nuna matukar damuwarsa kan kisan da aka yi wa matafiyan a ranar Juma’a, a lokacin da suka bata kan hanyarsu a yayin da suke tafiya don halartar wani daurin aure a karamar hukumar Mangu.
Ya ce, wadanda aka kashen, ba su dauke da wani makami, kawai suna kan hanyarsu ne ta zuwa daurin aure, wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari tare da kashe su, lamarin da ya jefa ‘yan uwan matafiyan cikin jimami.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp