• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mambobin Jam’iyyar NNPP 700 Sun Koma Jam’iyyar Labour A Adamawa

byMuh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
NNPP

A kalla mambobin jam’iyyar New Nigerian People’s Party (NNPP) dari bakwai, suka koma jam’iyyar Labour a jihar Adamawa.

Da take jawabi a madadin mutanen da suka canja shekar ranar Alhamis a Yola, Maryam Alhaji Sale, tace jam’iyyar Labour, itace jam’iyyar da zata fidda musu Kitse a wuta, don haka suka dawo jam’iyyar, daga jam’iyyarsu ta NNPP.

  • NNPP Ga Buhari: Ka Sanya Dokar Ta Baci A Jihohin Arewa 5

Da yake jawabin amsar mambobin jam’iyyar NNPP da suka canja shekar a Yola, dan takarar kujerar gwamna karkashin jam’iyyar Labour a jihar Umar Mustapha (Otumba Ekiti), yace jam’iyyar ta shigo jihar da haskenta, saboda haka shi zai ceto jama’ar jihar a babban zaben 2023.

Ya ci gaba da cewa “tarihi zai maimaita kansa a Adamawa, domin kuwa jam’iyar za ta amshe ragamar mulki a hannun jam’iyyar PDP a babban zaben 2023.

“Jam’iyyar Labor za ta kafa gwamnatin kowa da kowa, babu banbancewa tsakanin kabila ko addini, za kuma ta farfado da tattalin arzikin jiha, jama’a za su yi farin ciki da gwamnatin Labour fati” inji Otumba.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Haka kuma dan takarar kujerar gwamnan ya yabawa jama’ar jihar, bisa karban jam’iyyar Labour a matsayin jam’iyyarsu, yace sauran jam’iyyu sun kadu da zuwan jam’iyyar Labour duba da kwarewa da kuma nasarorin da dan takarar kujerar shugaban kasar jam’iyyar Peter Obi, ke dashi.

Yace “Peter Obi, shine daya telo cikin gwamnoni, da a karshen wa’adin mulkinsa ya bar naira miliyan dubu 70, da dalar Amurka miliyan 150, a lalitar gwamnatin jihar Anambara.

“A daidai lokacin da gwamnoni suke gina manyan gidaje, Peter Obi, alummarsa ya gina, ba kansa ba, wannan itace manufar jam’iyyar Labour” inji Otumba.

Da shima ke jawabi shugaban jam’iyyar Labour ta jihar Mista Nicolas Christopher, yace zuwan jam’iyyar fata ce ga jama’ar jihar, wacce ta zo da nufin kafa ingantacciyar gwamnati a kasa da jihar Adamawa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Karawa Dalibanta Kashi 50 Na Tallafin Karatu

Gwamnatin Kano Ta Karawa Dalibanta Kashi 50 Na Tallafin Karatu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version