• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah

by Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
in Labarai
0
Maniyyata Miliyan 1.2 Sun Iso Saudiyya Domin Hajjin Bana – Ma’aikatar Hajji Da Umrah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Hajji da Umrah na Ƙasar Saudiyya Tawfiq Al-Rabiah, ya sanar da zuwan maniyyata aƙalla miliyan ɗaya da dubu ɗari biyu, daga kasashe daban-daban na duniya wanda ya ce dukkan matakan tafiyarsu sun tafi lami lafiya kuma alhazan na cikin koshin lafiya.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a birnin Riyadh, Al-Rabiah ya jaddada kudirin Saudiyya na tabbatar da hidimta wa bakin Allah, tare da bayyana kokarin shugabanni na saukaka isar maniyyata zuwa masallatai biyu masu tsarki da kuma wurare masu tsarki, da tabbatar da gudanar da ayyukansu cikin sauki a kwanciyar hankali da samun kulawa.

  • Za A Yi Zaben Kananan Hukumomin Kebbi A Watan Agusta
  • Zimbabwe Ta Yaba Da Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Bangaren Makamashi Mai Tsafta Na Kasar

Ya kuma jaddada muhimmancin bin ka’idoji da umarni don tabbatar da cikakken hidima ga dukkan mahajjata, inda ya yi nuni da kaddamar da wani gangamin ƙasa da ƙasa don wayar da kan jama’a kan illar saɓa ka’idojin aikin Hajji, da ayyukan damfara wanda ake a ƙasashen duniya.

Kazalika gangamin da ake mai taken “Babu Hajji Ba Tare Da Izini Ba”, wanda ma’aikatar harkokin cikin gida ta Makka ke jagoranta, na da nufin wayar da kan jama’a tare da aiwatar da dokokin da suka tsara aikin Hajji, don tabbatar da dukkan maniyyatan sun kammala ibadarsu cikin kwanciyar hankali da lumana.

Al-Rabiah ya ce, sun dauki matakan zaɓar kamfanoni na musamman wajen karbar baki tare da kwararru don inganta yadda ake gudanar da aikin Hajji.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Ya ƙara da cewa a watannin da suka gabata, sama da ma’aikata da shugabannin kungiyoyin alhazai 120,000 sun samu horo cikin yaruka daban-daban na duniya.

Daga ƙarshe ya ce kasar Saudiyya ta yi amfani da duk wani abu da zai taimaka wajen ganin an samu nasarar aikin Hajji na shekarar 1445 bayan hijira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhazaiHajjin BanaSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Zaben Kananan Hukumomin Kebbi A Watan Agusta

Next Post

Wane Irin Tasiri Magudin Gwaje-gwaje Da Kamfanonin Samar Da Motoci Na Japan Suka Yi Zai Yi Ga Kasar?

Related

NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 hour ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

3 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

6 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

8 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

9 hours ago
Next Post
Wane Irin Tasiri Magudin Gwaje-gwaje Da Kamfanonin Samar Da Motoci Na Japan Suka Yi Zai Yi Ga Kasar?

Wane Irin Tasiri Magudin Gwaje-gwaje Da Kamfanonin Samar Da Motoci Na Japan Suka Yi Zai Yi Ga Kasar?

LABARAI MASU NASABA

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.