• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Kenya

Yayin da hadin gwiwa a fannin raya noma tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka ke kara bunkasa, sassan masu sana’ar noma a kasashen Afirka na kara gano dabaru, da cin gajiya daga kwarewar kasar Sin a fannin raya wannan sana’a mai dimbin tarihi. A baya bayan nan wasu bayanai sun nuna yadda manoman kasar Kenya dake gabashin Afirka, ke murna da shigar sabbin magungunan kashe kwari masu inganci na kasar Sin cikin kasuwannin kasar, matakin da aka shaida kyakkyawan tasirin sa ga kiyaye yabanyar da manoman kasar ke samu yayin girbi.

Masana a fannin lura da amfanin gona na cewa, fasahohin kasar Sin na raya sana’ar noma, musamman bangaren yaki da kwari masu lalata amfanin gona, sun kai matsayi daidai da na kasashen da suka ci gaba, a wasu fannonin ma sun zarce hakan.

  • Tsige McCarthy Daga Mukaminsa Ya Nuna Me Ake Nufi Da “Dimokradiyyar Amurka”
  • Jama’a A Fadin Kasar Sin Na Bikin Ranar Kafuwar Kasar Yayin Da Suka Shiga Lokacin Hutu Mai Tsawo

A bangaren inganci da wadatarwa, da rashin hadari ma, magungunan kashe kwari na Sin da ke shiga kasuwannin Kenya, sun kai matsayin nagarta na kasa da kasa, wanda hakan ya sanya suke ba da gudummawa wajen inganta tattalin arzikin manoman kasar.

Don haka muna iya cewa, yayin da Sin ke samun karin tagomashi a fannin bunkasa fasahohin raya noma a cikin gida, da samar da karin yabanya mai yalwa a duk shekara, a hannu guda kuma, fasahohin ta na kara shiga sassan nahiyar Afirka, inda suke taimakawa manoma cin karin gajiya daga sana’ar su.

Ko shakka ba bu wannan shi ne fatan al’ummun Afirka, wato hadin gwiwa domin cimma moriya tare da kasashe masu ci gaba a dukkanin fannoni, wanda kuma tuni kasar Sin ta wuce sahun gaba a wannan muhimmiyar tafiya. Kuma daya daga muhimman gabobin tafiyar shi ne inganta noma a Afirka, da aiwatar da dukkanin matakai na zamani, na tabbatar da samar da isasshen abinci da al’ummar nahiyar ke bukata. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Next Post
Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku

Kazakhstan, Kasa Marar Ruwa Mafi Girma A Duniya, Tana Da Nata Hanyar Shiga Teku

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.