• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Siyasa
0
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shekara ta 2024 ta kare, ‘yan Nijeriya sun ci karo da dimbin al’amuran siyasa da suka dabayyaye bangaren siyasar kasar a 2024. Tun daga sauye-sauyen siyasa zuwa fuskar diflomasiyya, ga wasu daga cikin manyan batutuwa 10 da suka mamaye siyasar Nijeriya a 2024 kamar haka:

Amincewa Da Sabon Taken Kasa

A wani yunkuri na inganta hadin kan kasa da kuma sanin manufofin kasar, gwamnatin Nijeriya ta maido da tsohon taken kasar na asali, wanda ake amfani da ita tun daga 1960 zuwa 1978.

  • Tsokaci A Kan Mazan Da Ba Su Yi Wa Matansu Kwalliya A Gida
  • Sabon Albashi: NLC Ta Fara Yajin Aiki A Jihohi 15 Na Nijeriya

Karin Mafi Karancin Albashi

Gwamnati ta kara mafi karancin albashi na kasa daga naira 30,000 zuwa naira 70,000 a matsayin martani ga tsadar rayuwa. Wannan shawarar ta biyo bayan tsawaita tattaunawa tsakanin kungiyoyin kwadago da jami’an gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Lalacewar Babban Tashar Wutar Lantarki

Rugujewar tashar wutar lantarki ta kasa ta nuna irin kalubalen da ake fuskanta a fannin samar da wutar lantarki a Nijeriya, wanda ke kawo cikas ga rayuwar yau da kullum ga miliyoyin ‘yan Nijeriya.

Gudanar Da Zanga-zangar Kamar Gwamnati Mara Kyau

Zanga-zangar dai ta barke a fadin kasar nan a cikin mawuyacin hali na tsadar rayuwa da kunci, lamarin da ‘yan Nijeriya suka dora alhakinsa kan sabbin sauye-sauyen da Shugaba Bola Tinubu ya yi. Akalla mutane 11 aka kashe, sannan an kama dan jarida daya.

Garambawul Ga Majalisar Manistoci

Shugaba Tinubu ya aiwatar da garambawul a majalisar ministocinsa, inda ya kori ministocin ilimi, yawon shakatawa, harkokin mata, da ci gaban matasa, da karamar ministar gidaje.

Zaben Shugaban Kasan Amurka

Zaben shugaban kasar Amurka na 2024 ya jawo hankulan ‘yan Nijeriya matuka, musamman saboda tasirin da manufofin ‘yan takara za su yi a Nijeriya.

Fashewar Bam A Ibadan

Wani abun fashewa da aka yi a garin Ibadan na Jihar Oyo, ya nuna baraka kan al’amuran tsaro, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama da kuma jikkata mutane masu dimbin yawa.

Garkuwa Da Daliban Kuriga

An yi garkuwa da dalibai sama da 200 da wani malami a garin Kuriga da ke Jihar Kaduna, amma daga baya aka sako su.

Turmutsutsun Rabon Kayan Tallafi A Ibadan Da Anambra Da Abuja

An samu turmutsutsu wajen rabon kayan tallafin Kirsimeti a Ibadan da Jihar Anambra da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja, wanda ya haifar da hasarar rayuka da jikkatar jama’a da dama, lamarin da ke nuna bukatar inganta matakan dakile cunkoson jama’a da kuma tsarin bayar da tallafin kayan abinci ko na kudi ko kuma na agajin gaggawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2024Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Da Ya Sa Legas, Abuja, Kaduna Suka Samu Masu Zuba Hannun Jari A Zango Na Uku

Next Post

NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

3 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

4 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

5 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa

NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.